By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Biyan kudaden jarabawar NBAIS – NAPAIS ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Biyan kudaden jarabawar NBAIS – NAPAIS ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano
News

Biyan kudaden jarabawar NBAIS – NAPAIS ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano

Attajdid
Last updated: 2025/11/04 at 1:53 PM
Attajdid Published November 4, 2025
Share
SHARE

Biyan kudaden jarabawar NBAIS – NAPAIS ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano

Kungiyar National Association of Proprietors of Arabic and Islamiyya Schools (NAPAIS) ta yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, bisa ci gaba da goyon bayansa da jajircewarsa wajen bunkasa ilimin addinin Musulunci a cikin jihar.

Yabon ya fito ne daga Shugaban Kungiyar na Arewa maso Yamma (North West Zonal Chairman), Malam Aliyu Ibrahim Sani Mainagge, a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Litinin, 3 ga watan Nuwamba, 2025.

A cewar Malam Mainagge, “Lallai ya kamata mu yaba wa Gwamnan Jihar Kano bisa irin kokarinsa da rashin gajiyawa wajen ganin cewa daliban da ke karatun Arabiyya da Addinin Musulunci suna da damar ci gaba da karatu cikin inganci.”

A zaman Majalisar Zartarwa ta Jiha da aka gudanar a ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025, majalisar ta amince da biyan kudi har ₦308,957,001.00 (Naira Miliyan Dari Uku da Takwas, Dubu Dari Tara da Hamsin da Daya) ga Hukumar Shirya Jarrabawar Arabiyya da Addinin Musulunci ta Ƙasa (NBAIS) domin a fitar da sakamakon jarrabawar daliban makarantun Arabiyya da Islamiyya, don ba su damar ci gaba da karatunsu na gaba da sakandare.

Malam Mainagge ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta ci gaba da irin wannan kokari mai albarka, yana jaddada cewa irin wannan mataki yana da muhimmanci wajen gina al’umma mai nagarta da ilimi.

Kungiyar National Association of Proprietors of Arabic and Islamiyya Schools (NAPAIS) ita ce ƙungiyar dake haɗa masu makarantun Arabiyya, Islamiyya da Tsangayu a duk faɗin Najeriya, domin ci gaban ilimin Musulunci da kyautata tarbiyyar al’umma.

Sa hannu:
Malam Aliyu Ibrahim Sani Mainagge
Shugaban Arewa Maso Islamiyya Schools (NAPAIS)

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid November 4, 2025 November 4, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Jam’iyyar NNPP wadda Dakta Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu ƙarfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon Gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.

Attajdid Attajdid May 16, 2025
SOKE YUNKURIN GYARA KUNDIN TSARIN MULKI DOMIN KARFAFA SHARI’AH DA MAJALISAR WAKILAI TA YI.
Jirgin Yakin Isra’ila ya Harbi Wani Jariri Dan Wata 6 a Gaza
Ta’addancin Isra’ila a Gaza:
Badakalar Milliyan N440 : Kotu Ta Rufe Asusun Kwankwaso
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?