A yau, ƙungiyar Hamas ta sanar da cewa ta cimma yarjejeniya da ke kawo ƙarshen yaƙin kisan kiyashi a Gaza, bayan tattaunawa mai zurfi da alhakin gaskiya da ta yi tare da sauran ƙungiyoyin gwagwarmaya na Palasɗinu, bisa shawarwarin Shugaba Donald Trump da aka gudanar a Sharm al-Sheikh.
Hamas ta bayyana cewa wannan yarjejeniya ta haɗa da dakatar da yaƙin gaba ɗaya, janyewar dakarun Isra’ila daga Gaza, shigar da kayan tallafi, da musayar fursunoni tsakanin ɓangarorin biyu.
A cikin sanarwar, ƙungiyar ta yaba da rawar da ƙasashen Qatar, Masar, da Turkiyya suka taka wajen shiga tsakani, tare da jinjinawa ƙoƙarin Shugaba Trump na Amurka don tabbatar da hakar zaman lafiya da janyewar mamaya gaba ɗaya daga Gaza.
Hamas ta kuma roƙi Amurka, ƙasashen masu shiga tsakani, da sauran ƙasashen Larabawa da Musulmi su tabbatar da Isra’ila ta aiwatar da yarjejeniyar ba tare da jan kafa ko ƙeta alkawari ba.
Ƙungiyar ta godiya ga al’ummar Palasɗinu a Gaza, Kudus, Yamma, da ƙasashen waje bisa jajircewa da sadaukarwa, tana mai cewa irin waɗannan jarumta ne suka gaza da shirin Isra’ila na tilasta ƙauracewa da mallakar ƙasa.
A ƙarshe, Hamas ta jaddada cewa jinin shahidai da sadaukarwar jama’a ba za su tafi a banza ba, tana mai tabbatar da cewa za su ci gaba da fafutuka har sai Palasɗinu ta samu ’yanci da cikakken ikon kai.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




