Gwamnatin Jihar Sokoto ta ƙaddamar da wani sabon shiri na tilasta wa duk ma’aikatan lafiya da gwamnati ta ɗauki nauyin karatunsu yin aikin shekara biyu a yankunan karkara bayan kammala karatu.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Abubakar ne ya bayyana hakan, inda ya ce wannan mataki zai shafi likitoci, nas-nas, ma’aikatan da ke lura da bayar da magunguna da sauran jami’an lafiya.
Ya bayyana cewa wannan mataki wani yunkuri ne na cike gibi da ake fama da shi a yankunan karkara dangane da ƙarancin ma’aikatan lafiya.
A cewarsa, gwamnati ta yi binciken bukatuwar karin maaikatan, wanda ya nuna akwai babban gibin rabon ma’aikatan lafiya tsakanin birane da karkara.
Kwamishinan ya ƙara da cewa za a ba wa waɗanda aka tura kauyuka ƙarin alawus na kashi 10 cikin 100 a albashinsu, tare da samun sabbin kayan aiki da tsaro da aka inganta domin sauƙaƙa musu aiki.
Mai Rahoto
Nura Abubakar Musa




