By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Kan Jami’an Tsaron Isra’ila Ya Rarrabu Akan Yakin Gaza
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Kan Jami’an Tsaron Isra’ila Ya Rarrabu Akan Yakin Gaza
International News

Kan Jami’an Tsaron Isra’ila Ya Rarrabu Akan Yakin Gaza

Attajdid
Last updated: 2025/09/17 at 9:22 AM
Attajdid Published September 17, 2025
Share
SHARE

Kungiyar UNICEF ta bayyana cewa yara a Gaza na cikin mawuyacin hali sakamakon matsanancin yunwa. Rahoton kungiyar ya nuna cewa yaro ɗaya cikin kowadan ne yara biyar na fama da rashin abinci mai gina jiki cikin tsanani, abin da ke nuna tsananta matsalar a cikin sauri fiye da yadda aka saba gani.

 

A wani mataki na diplomasiyya, ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta fito da sanarwa tana Allah-wadai da tsananta hare-haren Isra’ila a tsakiyar Gaza. Faransa ta bayyana cewa wannan kamfen ba shi da hujjar soja, tare da kira ga Isra’ila ta dakatar da shi, sannan a dawo da tattaunawa cikin gaggawa domin kawo karshen tashin hankali.

 

Daga cikin Isra’ila kuwa, gidan talabijin Channel 12 ya rawaito cewa tsoffin shugabanni da ma’aikata kusan 260 daga hukumar tsaron cikin gida, wato Shabak, sun fito da adawa da nadin David Zini a matsayin sabon shugaban hukumar. Wannan ya nuna rarrabuwar kai cikin tsarin tsaron kasar.

 

A gefe guda, jaridar The Economist ta ruwaito cewa babban hafsan sojin Isra’ila ya sha fadawa gwamnati cewa da wuya a samu nasara ta karshe kan Hamas, kuma wannan yaki na iya ɗaukar shekaru. Sai dai rahoton ya nuna cewa shugaban Amurka na baya, Donald Trump, na fara gajiyawa da wannan rikici, duk da cewa Firayim Minista Benjamin Netanyahu ya sha tabbatar masa cewa harin Gaza zai zama bugun karshe kan Hamas. Idan ba haka ba, jaridar ta yi hasashen cewa Trump na iya matsawa Isra’ila ta dakatar da yaki.

 

Haka kuma, jaridar Politico ta bayyana cewa wani babban kamfani da ke kula da harkokin jama’a ya soke kwangila da gwamnatin Isra’ila. Wannan kwangilar dai ta shafi yada ra’ayinta da kare kanta a idon duniya kan rikicin Gaza.

 

A karshe, Hukumar tsaron cikin gida ta Isra’ila ta tabbatar da cewa kararrawar gargadi ta tashi kusa da filin jirgin saman Ramon da ke arewacin Eilat. Wannan ya faru ne bayan da aka gano wani jirgi mara matuki ya kutsa cikin yankin.

 

 

Mai rahoto;

M.B.S.Gama.

 

 

At-tajdid News.

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid September 17, 2025 September 17, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Since 2012, there have been countless incidents of physical and verbal assaults against priests and other clergy, attacks on Christian churches

Attajdid Attajdid December 10, 2024
Matsayar Gungiyar Hamas da Dakarun Mukawama Akan Yarjejeniyyar Tsagaita Wuta a   Yakin da ake yi a Palestine
‘Yan Sandan Najeriya Sun Tarwatsa Masu Zanga-zanga a Abuja
GOV. LAWAL PRESENTS N545 BILLION 2025 ‘RESCUE BUDGET 2.0’ TO ZAMFARA ASSEMBLY, PRIORITIZES SECURITY, HEALTH AND EDUCATION
FG, FMAN Supports 160,000 Wheat Farmers In Jigawa
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?