ISWAP ta ɗauki alhakin harin Marte
Ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin babban hari kan sansanin sojin Najeriya da ke garin Marte a jihar Borno.
Cikin wani sako da ƙungiyar ta wallafa a shafinta na Telegram ta ce mayaƙanta sun far wa sansanin sojin gabanin asubahin ranar Litinin.
Tana mai cewa mayaƙan nata sun yi arangama da sojojin har na tsawon sa’a guda, kafin su yi nasarar ƙwace sansanin, tare da kashe sojoji masu yawa lamarin da ta ce ya ”tilasta wa wasu tserewa”.
Harin shi ne na baya-bayan nan a jerin hare-haren da mayaƙan suka kai garuruwan Marte da Dikwa da kuma Rann da kuma Gajiram, inda aka rasa rayukan da ba a kai ga ƙiyasta su da asarar dukiyoyi masu yawa tare da sace makamai.
BBC Hausa
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




