Rundunar Sojin Najeriya karkashin operation fansan yamma tta tabbatar da mutuwar sojoji biyar a wani harin kwantan bauna da ‘yan ta’adda suka kai a hanyar Lilo zuwa Kotorkoshi, a karamar hukumar Gusau, Jihar Zamfara.
Lamarin ya faru ne a ranar Litinin, yayin da sojojin ke rakiyar ‘yan kasuwa zuwa kasuwar Gusau.
Rahotanni sun ce sojoji biyar sun rasa rayukansu, yayin da aka kashe wasu daga cikin ‘yan ta’addan a fafatawar da akayi.
A cikin wata sanarwa da , mai magana da yawun rundunar soji a jihar, Kyaftin David Adewusi, ya ce dakarun 1 Brigade daga sansanin Lilo sun fuskanci luguden wuta daga ‘yan ta’adda yayin da suke sintiri a yankin Lilo zuwa Kofi.
Kyaftin Adewusi ya ce harin kwantan baunar na cikin ci gaba da farmakin da ake yi da nufin murkushe ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a yankunan Zamfara da Sokoto.
A cewarsa, daga ranar 8 zuwa 10 ga watan Satumba, dakarun soji sun kama kayan aikin ‘yan ta’adda, ciki har da kudin fansa da suka kai sama da naira miliyan ashirin.
Sannan sun kwato dabbobi fiye da dari da sittin da aka sace, tare da kashe wasu daga cikin ‘yan ta’addan.
Ayyukan sun shafi yankuna kamar Shinkafi, Gusau, Bukkuyum da Tureta, inda aka lalata maboyar ‘yan ta’adda a dazuka, yayin da wasu daga cikinsu suka tsere da raunukan harbi.
Rundunar sojin ta ce za ta ci gaba da wannan farmaki har sai an tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.




