By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Ƙoƙarin gwamnatin Nijeriya na sulhunta NUPENG da Dangote ya ci tura
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Ƙoƙarin gwamnatin Nijeriya na sulhunta NUPENG da Dangote ya ci tura
News

Ƙoƙarin gwamnatin Nijeriya na sulhunta NUPENG da Dangote ya ci tura

Attajdid
Last updated: 2025/09/09 at 7:41 PM
Attajdid Published September 9, 2025
Share
SHARE

Ƙoƙarin gwamnatin Nijeriya na sulhunta NUPENG da Dangote ya ci tura

Ƙungiyar NUPENG ta yi shelar cewa za ta fara yajin aiki daga ranar Litinin, 8 ga watan Satumbar shekarar 2025, kan zargin da ta yi wa kamfanin Dangote cewa yana ɗaukar matakan da suka saɓa wa dokokin ƙwadago.

Zaman sirrin da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta gudanar ranar Litinin da maraice domin sulhuta ƙungiyar ma’aikatan dakon man fetur da gas (NUPENG) da kamfanin mai na Dangote ya kasa cim ma nasara.

 

 

Rahotanni daga Nijeriya sun ce zaman da Ministan Ƙwadagon ƙasar, Mohammed Dingyadi, da Ƙaramar Ministar Ƙwadago, Nkiruka Onyejeocha, suka jagoranta wani mataki ne na warware taƙaddamar da ke tsakanin ɓangarorin biyu domin kauce wa yajin aikin da ƙungiyar NUPENG ta ce za ta yi.

 

Waɗanda suka halarci zaman sun haɗa da shugabannin ƙungiyar NUPENG da jami’an ƙungiyar ƙwadagon Nijeriya (NLC) da kuma na ƙungiyoyin ƙwadago na TUC.

Kazalika zaman ya samu halartar babban daraktan ajiya da rabawa da sayar da mai na hukumar da ke kula fannin tacewa da sayar da mai ta Nijeriya (NMDPRA), Ogbugo Ukoha, da kuma wakilan kamfanin Dangote da gidan man MRS.

 

Sai dai an kammala taron ba tare da cim ma matsaya ba game da taƙaddamar da ake yi tsakanin NUPENG da Matatar Mai ta Dangote.

 

Ranar Juma’ar da ta gabata ne dai ƙungiyar ƙwadagon NUPENG ta yi shelar ƙaddamar da yajin aiki daga ranar 8 ga watan Satumba kan abin da ta kira ƙoƙarin Matatar Man Dangote na hana direbobin tankokin dakon mai na CNG ɗinsa shiga ƙungiyoyin ƙwadago.

Duk da cewa ƙungiyoyin ƙwadagon direbobin tankokin dakon mai na PTD da DTCDA sun nesanta kansu da wannan matakin, NUPENG ta tabbatar ranar Lahadi cewa za ta tsunduma cikin yajin aikin.

 

 

Domin ta kauce wa wannan yajin aikin, gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadagon ranar Lahadi ta sake tunani kan wannan matakin nata.

 

Dingyadi, a wata sanarwar da shugabar sashen sadarwa ta ma’aikatarsa, Patience Onuobia, ta fitar, ya yi kira ga NUPENG ta dakatar da yajin aikinta domin ba da damar tattaunawa.

Ministan na Ƙwadago ya kuma yi kira ga NLC ta janye shawarar da ta bai wa ƙungiyoyin da take da alaƙa da su na kasancewa cikin shirin shiga yajin aikin goyon bayan NUPENG kan abin da ta kira “matakan ƙin jinin ma’aikata da ƙungiyoyin ƙwadago” na kamfanin Dangote.

 

Ministan ya ce, “na kira duk masu ruwa da tsaki domin wani zaman sasantawa ranar Litinin 8 ga watan Satumba na shekarar, 2025. Tun da na riga na sa baki, na roƙi NUPENG ta janye matakin da ta ɗauka na rufe fannin man fetur daga gobe” .

 

“Fannin man fetur na da humimmi ga wannan ƙasar. Ya ƙunshi asalin tattalin arziƙin ƙasar. Yajin aiki , ko na rana ɗaya ne, zai yi tasiri mai muni, da zai janyo asarar biliyoyin naira da kuma wahala mai tsanani ga ‘yan Nijeriya,” in ji ministan.

 

Mai rahoto

Mustapha Garba Usman

You Might Also Like

Nursing Mother Inmate Freed as Jigawa NLC Women’s Wing Clears Her Court Fines

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

Attajdid September 9, 2025 September 9, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

NIJERIYA TA ZARGI WANI KAMFANIN KASAR CHINA DA KOKARIN KWACE KADARORIN GWAMNATI.

Attajdid Attajdid August 16, 2024
Mohamed Salah ya zama gwarzon ɗan wasan Gasar Firimiya a kakar bana
Protest: Jigawa APC Urged Youth Not be Agent Of National Destruction.
FG, FMAN Supports 160,000 Wheat Farmers In Jigawa
SHUGABAN KASA BOLA TINUBU DA GWAMNONIN JIHOHI SUN DAKATAR DA BAWA ƙANANAN HUKUMOMI ‘YANCI CIN GASHIN KANSU
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?