Rundunar ‘Yan sanda a Jahar Kano ta gurfanar da mutane 333 da ake zargi da Bangar Siyasa a cikinsu kuma har da wasu Jami’an gwamnati da aka cafke su na kokarin tada tarzoma ayayin zaben cike gurbi na majalisar dokokin tarayya na ranar Asabar, a kananan hukumomin Ghari da Bagwai da kuma shanono.
Kwamishinan ‘Yan sandan Jahar kano Ibrahim Adamu Bakori ya bayyana hakan a hedikwatar Rundunar ‘Yansanda da ke a Bompai.
A cewar Kwamishinan ‘Yan sandan Jahar kano wadanda ake zargin an gurfanar da su a gaban kotunan majistare daban-daban akan laifukan da su ka hadar da hada kai a tafka laifi da mallakar makamai da barazana da kwace da kuma lalata kayan zabe.
Hakanan a wani labarin makamancin hakan, a can ma Jahar Ogun Rundunar ‘Yan sanda ta bayyana cewa ta cafke wasu mutane 10 da ake zargin ‘Yan Kungiyar Asiri ne da su ka yi kokarin haifar da tsaiko a yayin zabe a jahar ta Ogun.
A bayabayannanne dai lauyannan da ke rajin kare Hakkin Dan Adam Femi Falana ya ce berkewar rikice-rikice da kuma aiyukan daba da su ka dabaibaye zabukan cike gurbi a fadin Nigeria ya tabbatar da hukuncin kotun kasar Canada da ya Ayyana manyan Jam’iyyun Siyasar Nigeria na PDP da Kuma APC a matsayin Kungiyoyin ‘Yan ta’adda.




