Ma’aikatar gidaje da ci gaban birane ta tarayya ta gargadi ‘yan Najeriya da su yi hattara da ‘yan damfara da ke neman cin gajiyar gidaje 753 da EFCC ta kwace kuma aka mika wa gwamnatin tarayya.
Idan ba a manta ba a watan Mayun 2025 ne hukumar EFCC ta mika wadannan gidaje ga gwamnatin tarayya, inda ministan gidaje, Ahmed Dangiwa, ya bayyana cewa gwamnati za ta sayar da gidajen ga jama’a ta hanyar tsari na gaskiya da adalci, bisa manufar tsarin nan na Renewed Hope Agenda.
Cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar, Badamasi Haiba, ya fitar a Abuja ranar Asabar, ma’aikatar ta tabbatar da cewa bata amince da wani mutum ko kamfani ya yi katsalandan wajen sayar da gidajen ba.
Ta yi kira ga jama’a da su yi ta-ka-tsan-tsan, su kuma jira cikakken tsarin sayar da gidajen da gwamnati za ta sanar a hukumance.




