Rundunar yan sandan jihar Gombe ta cafke wasu matasa biyu da ake zargi da kashe wani matashi mai suna Dauda Ahmed dan shekara 22 a garin Kumo da ke karamar hukumar Akko a jihar.
A cewar rundunar yan sandan wadanda ake zargin Babayo Musa mai shekaru 20 da kuma Zaidu Sani mai shekaru 18, ana tuhumar su ne da hada baki da wasu mutane biyu.
Lamarin ya faru ne da safiyar ranar Talata a unguwar Jauro Musa, inda rahotanni suka ce an yi wa mamacin kwanton bauna tare da yi masa munanan raunuka a kai da kuma cikinsa.
An garzaya da shi babban asibitin Kumo, Wanda kuma isarsu keda wuya aka tabbatar da rasuwarsa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai, ya ce rundunar ta yi Allah wadai da wannan aika-aika tare da gargadin jama’a da su guji aikata laifukan ta’addanci.
Ya kara da cewa ana ci gaba da kokarin damke sauran mutane biyun wadanda ake zargin da suka hada da Sulaiman da Usama.




