A cikin tsokaci mai tsanani kan mummunan rashin tsaro da ake fuskanta a Jihar Zamfara, fitaccen malamin addinin Musulunci Farfesa Mansur Sokoto ya bayyana a fili yadda Gwamnan Dauda Lawal ke gudanar da lamuransa, yana zargin cewa ya yi sakaci da nauyin da ke kansa kuma yana daura laifin ga wasu mutane Daban.
A cikin wani bidiyo na baya-bayan nan, Farfesa Sokoto tare da wasu malaman addini, sun kira gwamnan da ya dauki mataki mai karfi kan hare-haren ‘yan ta’adda da ke ci gaba da kashe rayuka da korar al’ummomi daga mazaunansu.
Matsalar tsaro a Zamfara ta kasance.matsala mai muni, Wadda kungiyoyin ‘yan ta’adda, ciki har da masu tsattsauran ra’ayi Fulani, suke kai hare-hare suna kashe mutanen da ba su ji ba su gani ba. Adadin kisan gillar ‘yan ta’adda a Najeriya ya kasance mai girma, inda aka kiyasta rasuwar mutane 4,020 a cikin watanni goma na farkon shekarar 2022.
Sokoto ya jaddada cewa Gwamnan Lawal, ya san da rikicin tun kafin lokacin da ya hau kan karagar mulki, Don haka ba Wani uzuri dole Gwamnan ya nuna shugabancin da ake bukata wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan jihar. Duk da kokarin Lawal na baya-bayan nan na kafa Asusun Tsaro na Jihar mai mambobi 21 da halartar tattaunawar tsaro ta yankin, Sokoto ya nace cewa wadannan matakai basu isa ba wajen samar da cikakkiyar Mafita da ake bukata gaggawar magance kalubalen Matsalar Tsaron Zamfara shi ne mafi aala fannoni.
Mutanen Zamfara, da suka tsinci kansu a tsaka mai wuya da karuwar tashin hankali, suna bukatar a dauki matakin da ya dace, ba kawai maganganu ba. Sokoto ya jaddada cewa lamarin na bukatar cikakken lissafi daga Gwamnan Lawal don fifita jin dadin da tsaron mutanensa.
“Ya kamata ka daina zargi da kukawa game da wanda ya rike mukamin kafin ka. Idan kuka ya yi yawa, za a iya daukarka a matsayin mace,” in ji Sokoto.




