Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayar da gudunmawar kudi kimanin Naira miliyan 5 da fili ga kowanne daga cikin iyalan ‘yan wasa 22 da suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a lokacin da suke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta kasa a jihar Ogun.
Yan wasan da suka wakilci Kano a watan Yunin bana sun samu lambobin zinare shida, da azurfa 13, da tagulla 10 kafin rasuwarsu a garin Dakatsalle da ke karamar hukumar Bebeji mai tazarar kilomita 50 daga Kano.
Wadanda suka rasun sun hada da ’yan wasa, kociyoyi, dan jarida, ma’aikatan lafiya, direbobi da kuma makanikai.
Mai baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf shawara kan dabarun yada labarai, Ibrahim Adam, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ta shafin Facebook a ranar Laraba.
Nura Abubakar Musa
At’tajdid News




