By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
News

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Attajdid
Last updated: 2025/06/20 at 4:57 PM
Attajdid Published June 20, 2025
Share
SHARE

Gwamnatin ta ce ba rauni ne ya sa za ta yi sulhu da ‘yan bindiga ba.

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce ba gazawa ba ce ta sa ta yanke shawarar tattaunawa da ’yan bindigar da suka yanke hukuncin ajiye makamansu ba.

 

Ta ce wannan hanya ce mafi kyau da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Basharu Altine Guyawa, ya soki wannan mataki na gwamnatin.

 

Amma Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara kan Tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya ce manufar gwamnati ita ce ta kawo zaman lafiya, ba don ta kasa ba.

 

Ya ce, “Mun san kowa na da ‘yancin faɗin albarkacin bakinsa. Amma dole ne mu fayyace dalilin da ya sa Gwamna Ahmed Aliyu ke amfani da hanyoyi daban-daban wajen magance matsalar rashin tsaro, ciki har da tattaunawa da ‘yan bindigar da suka tuba.”

 

Ya ƙara da cewa abin mamaki ne yadda Guyawa ke sukar wannan yunƙuri.

 

Ya ce shi ma ya taɓa buƙatar shirin shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga domin yin sulhu.

 

Kanal Usman ya bayyana cewa gwamnati tana amfani da dukkanin matakai biyu; na ƙarfi da na sulhu.

 

A cewarsa, mutane da yawa a Rabah, Goronyo, Isa, Sabon Birni da wasu yankuna na ta yin hijira.

 

Manoma sun bar gonakinsu, amfanin gona ya ragu, kuma kasuwanci ya tsaya cak.

 

Wannan ya jawo ƙarancin abinci da tsadar rayuwa a faɗin jihar.

 

“Burinmu shi ne mu dawo da zaman lafiya, mu dawo da mutane gidajensu, sannan a sake farfaɗo da harkokin noma da kasuwanci,” in ji shi.

 

Ya ce har yanzu gwamnati na aike jami’an tsaro inda ya dace.

 

Amma waɗanda suka tuba da gaske za a karɓe su bisa kulawa da tsari na gyaran hali.

 

“Wannan ba gajiyawa ba ce ko jin tsoro, wannan dabara ce ta sulhu domin ɗorewar zaman lafiya.”

 

Amma ya roƙi masu sukar gwamnati da su yi magana cikin hankali.

 

“Jihar Sakkwato na buƙatar haɗin kai da mafita, ba rabuwar kai da zargi ba. Gwamna Ahmed Aliyu na aiki tuƙuru don kawo zaman lafiya.”

 

Mai Rahoto

Mustapha Garba Usman

 

Attajdid news

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid June 20, 2025 June 20, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Rahotanni daga Palasɗinu sun bayyana cewa Isra’ila ta kai wani sabon hari a Zirin Gaza da nufin kashe kakakin rundunar Hamas, Abu Obaidah

Attajdid Attajdid August 30, 2025
An Rantsar da Fafaroma 14 Leo
Jama’atut Tajdidil Islamy Ka”id Kano Lost Elder Brother 
PROUD MOMENT FOR MSSN AS NIGERIA EMERGES 2nd AT AL- FOURQUANE Int’l QUR’ANIC  COMPETITION IN COTE D’ AVOIR
Hamas ta Bayyana Sunayen Isra’ilawa uku da za ta Saki Gobe Asabar
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?