Har Yanzu Kungiyar Hamas Tana da Karfi a Yakin da Take Gwabzawa da Yahudawan Israel
A wani rahoto da Aljazeera ta fitar yana nuna har yanzu Hamas na da daruruwan rokoki, amma ta kauracewa harba su saboda fargabar cutar da fararen hula da kuma dakaru masu dauke da makamai daga kungiyoyi daban-daban a Zirin Gaza. Dadin-dadawa, har yanzu akwai faffadan hanyoyin sadarwa a zirin Gaza, wadanda suka fi maida hankali a birnin Gaza, da Khan Yunis, da kuma sansanonin tsakiya.
A wani harin bam da Isra’ila ta kai kan wata makaranta dake zama mafaka a unguwar Al-Daraj da ke birnin Gaza ya yi sanadiyar mutuwar kusan mutane 19.
Ministan Harkokin Wajen Spain ya shaidawa Al Jazeera, amincewa da kasar Falasdinu shi ne matakin farko na samun zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Daga rahotan da At-tajdid News take samu daga kasashan Turai jami’an tsaro na ci gaba da muzgunawa masu nuna goyan Palasdinawa, misali; jami’an tsaro a cibiyar Barclays dake birnin New York, inda ake gudanar da bikin kaddamar da jami’ar Brooklyn, sun muzgunawa wadanda suka kammala karatunsu da suke nuna goyon bayan Falasdinu ta hanyar cire alamu na Falasdinawa da suke sanye da su tare da cire su daga bikin.
Da kuma ci gaba da zanga-zangar neman kawo karshen yakin Gaza a wasu manyan biranen duniya da suka hada da babban birnin kasar Faransa, Paris, an sake yin zanga-zangar nuna rashin amincewa da harin bam da Isra’ila ke kaiwa Gaza tare da neman kawo karshen yakin.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




