Ko ECOWAS za ta iya jure wa ƙalubalen da ke gabanta?
Yayin da take cika shekara 50 da kafuwa, ana iya cewa ECOWAS ta fuskanci faɗi-tashi da dama da kuma jerin nasarori da ƙalubale tamkar dai wani mutum da shekarunsa suka fara nisa.
“Sau tari ba mu godiya kan nasarorin da muka samu,” Inji ministan harkokin wajen Najeriya Ambasada Yusuf Tuggar.
An fara tunanin kafa ƙungiyar ta ƙasashen yammacin Afirka ne bayan shugabannin yankin sun fara hangen yadda za su dunƙule waje guda domin ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.
A ranar 28 ga watan Mayun 1975, aka kafa ƙungiyar bunkasa tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS) lokacin da shugabannin ƙasashen yankin suka sanya hannu kan yarjejeniyar kafa ta a Lagos.
Ƙudirin su kakkyawar fata ce- inganta alaƙar kasuwanci da bunƙasa hada-hadar jama’a da kuma tabbatar da zaman lafiya da tsaro.
Jama’ar yankin dai sun fuskanci abubuwa da dama masu kamanceceniya da suka haɗa da cinikin bayi da yanka kan iyakoki da Turawan mulkin mallaka suka yi da kuma rashin ci gaba, waɗanda sa nan da nan suka yi amanna da tunanin kafa ƙungiyar.
Sai dai kuma yayin da ECOWAS ke cika shekara 50 da kafuwa, dambarwar siyasa da ta ke fama da ita na nuni da tangaɗin da makomar ta ke yi
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




