‘Hare-hare ta sama da Isra’ila ke kai wa sun fi razana ni’
Wata ƴar Isra’ila da aka yi garkuwa da ita a Gaza ta ba da labarin abin da ya rinka tsorata ta, a lokacin da take hannun Hamas, tana mai shaida cewa hare-haren sama da Isra’ila ke yi sun fi razanata.
Naama Levy, ta faɗa wa ƴan jarida a birnin Tel Aviv a taron dandazon mutanen da ke kiran a dawo da sauran ƴan ƙasar da ake garkuwa da su cewa, tana fargabar rayukan sauran mutanen.
Ta ce a duk lokacin da ta ji karar bam tana sake tabbatarwa kanta cewa babu tantama karshenta ya zo.
Yayin da Isra’ila ke ci gaba da hare-hare babu ƙaƙƙautawa a Gaza, sojojin ƙasar sun ce suna nazarin rahotonni da ke cewa harin nasu ya kashe yara tara ƴan gida ɗaya.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




