By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Masu Shiga Tsakani Sun Samu ci-gaba a Tattaunawar Tsagaita Wuta a Gaza, Amma har Yanzu ba a Cim ma Matsaya ba
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Masu Shiga Tsakani Sun Samu ci-gaba a Tattaunawar Tsagaita Wuta a Gaza, Amma har Yanzu ba a Cim ma Matsaya ba
International News

Masu Shiga Tsakani Sun Samu ci-gaba a Tattaunawar Tsagaita Wuta a Gaza, Amma har Yanzu ba a Cim ma Matsaya ba

Attajdid
Last updated: 2025/01/10 at 6:13 AM
Attajdid Published January 10, 2025
Share
SHARE

Majiyoyin Falasɗinawa da ke da masaniya kan tattaunawar da ake yi sun ce Amurka da masu shiga tsakani na Larabawa sun samu ci-gaba a yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, amma ci-gaban bai kai yadda za a cim ma matsaya ba.

 

Yayin da ake ci gaba da tattaunawar a Qatar, sojojin isra’ila sun kai hare-hare a faɗin yankin Falasɗinu da aka mamaye, inda suka kashe aƙalla mutane 17, a cewa cibiyoyin lafiya na Falasɗinu.

 

Kashe-kashen sun kawo adadin waɗanda hare-haren Isra’ila suka yi sanadiyyar mutuwarsu zuwa 70 a faɗin Gaza cikin sa’o’i 24, kamar yadda ma’aikatar lafiyar yankin ta bayyana.

 

Qatar da Amurka da Masar suna wani gagrumin yunƙuri na ganin an cim ma matsaya don dakatar da yaƙin da Isra’ila take yi a Gaza da kuma sakin ragowar mutanen da aka yi garkuwa da su kafin Joe Biden ya bar ofis.

 

Shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump ya yi gargaɗin cewa “za a ga balbalin bala’i” idan ba a saki mutanen da aka yi garkuwa da su ba zuwa lokacin da za a rantsar da shi ranar 20 ga Janairu.

 

A ranar Alhamis, jami’an Falasɗinawa da ke kusa da tattaunawar sun ce, rashin cin ma matsaya kawo yanzu ba ya nufin cewa tattaunawar ba ta kai ko ina ba, kuma wannan ne yunƙurin da ya fi kowanne mayar da hankali kawo yanzu.

 

“Akwai muhimmiyar tattaunawa da ake yi, masu shiga tsakani da masu tattaunawa suna yin magana sosai akan kowace kalma da kowane batu. An samu nasara idan aka duba yadda aka warware wasu batutuwa da suka zama kiki-kaka a baya, amma dai har yanzu ba a cim ma matsaya ba,” kamar yadda ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters ba tare ƙarin bayani ba.

 

An shafe fiye da shekara guda ɓangarorin biyu sun maƙale a wajen ɗaya kan muhimman batutuwa biyu.

 

Hamas ta ce za ta saki sauran fursunonin ne kawai idan Isra’ila ta amince da kawo ƙarshen yaƙin ta kuma janye duka sojojinta daga Gaza.

 

 

Mai rahoto;

M.B.Gama.

 

 

At-tajdid News.

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid January 10, 2025 January 10, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

DICON @60: MATAWALLE HAS ANNOUNCED THE UPCOMING CELEBRATION OF THE DEFENCE INDUSTRIES CORPORATION OF NIGERIA (DICON) 60th ANNIVERSARY.

Attajdid Attajdid August 12, 2024
SOJOJIN ISRA’ILA SUNA CIGABA DA KAMA FALASDINAWA
Triumph Furious As Dollar Crashes In Market Reserves
Gwamnatin Jihar Jigawa ta dauki nauyin dalibai 184 domin karo karatun likitanci a kasashen waje.
Yan Nigeria sun koka akan barazanar da suke fuskanta a African ta kudu
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?