By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: TIRKA- TiRKAR SABUWAR DOKAR HARAJi
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > Uncategorized > TIRKA- TiRKAR SABUWAR DOKAR HARAJi
Uncategorized

TIRKA- TiRKAR SABUWAR DOKAR HARAJi

Attajdid
Last updated: 2024/12/03 at 11:29 AM
Attajdid Published December 3, 2024
Share
SHARE

Jiya nayi alkawarin zan tofa albarkacin bakina akan wasu kudurorin dokoki da shugaba Bola Ahmed Tinubu.ya gabatarwa majalisar dokoki ta kasa. An gabatar da wadannan dokoki don a yi wa fasalin harajin kasa garanbawul.

 

Wasika PBAT ya aikewa shugaban majalisar dattijai Sanata Godswill Akpabio kwafinsa. Sannan aka aikewa shugaban majalisar wakilai Dr Tajuddin Abbas nasa kwafin. A bisa ka’idar aikin majalisun za a zo da takardar gaban ‘yan majalisa a daga murya a karanta kowa ya ji. Idan an karanta shi ne abin da ake cewa ” An yi karatun farko wato First Reading.

 

Tun kafin a zo nan wajen a ranar 30 ga watan Oktoba 2024 a wani zama na majalisar tattalin arziki ta kasa, National Economic Council, wannan zauren ya kunshi duk gwamnoni na jihohi 36 da kuma ministan Abuja. Haka majalisar ta kunshi gwamnan babban banki CBN da minstocin kudi da kasafi da tsare-tsare, kuma shi wannan zauren yana karkashin mataimakin shugaban kasa. Atiku Abubakar ya taba rikewa, Farfsea Yemi Osinbajo ya rike shi, yanzu kuma yana hannun Kashim Shattima. Kundin tsarin mulki shi ya baiwa mataimakin shugaban kasa wannan iko. Aikinsa kawai ya baiwa shugaban kasa shawara ta tattalin arziki, Amma aiki da shawarin ba lallai ba kuma tilas. A wannan zaman an gayyyaci Taiwo Oyedele, wato Chairman Presidential Committee on Fiscal Policy and Tax Reforms babban muhutin haraji kuma shugaban kwamitin Dabarun tara kudi da sarrafa su domin ya wayar da kan gwamnoni mai ke kunshe cikin maganar haraji. Haka an gayyyaci Zacceus Adedeji shugaban hukumar tara kudin haraji ta kasa wato FIRS duk a wannan rana. A wajen wannan zama ne aka zartar cewa a gaya wa shugaban kasa ya jingine wadannan dokoki har sai an sake duba su sarai, an yi shawara. Gwamnan jihar Oyo, wanda Bayerabe ne kuma dan jam’iyyar PDP Seyi Makinde shi ne ya yi magana a madadin duk gwamnoni.

 

Amma kuma tun kafin wannan ranar a karkashin kungiyar gwamnoni na arewa Northern Governors Forum NGF da manyan sarakunan yankunansu sun hada baki guri guda cewa ba su gamsu da akasarin tanadin da ke kunshe cikin wadannan sabbin dokokin da ake son zartaswa ba. A wannan taron da aka yi a Kaduna ranar 23 ga Oktoba 2024 gwamnan jihar Gombe, Alhaji Yahaya Inuwa dan jamiyyar APC shi ne ya fadawa duniya matsayin da suka dauka a dunkule.

 

Ai kuwa a yammacin ranar da NEC ta zauna ta ce a janye wannan kudurorin daga zauren majalisar har sai an yi kwaskwarima, Bayo Ononuga, mai baiwa shugaban kasa shawara akan labarai ya fito fili ya ce , duk wanda yake da wata magana ya tafi majalisar kasa, a can za a yi muhawara, duk inda ake da bukatar gyarawa a bi wannan tsarin sai a gyara. Kalmomin Bayo basu yi wa gwamnoni da sarakai da wasu shugabanni da ‘yan siyasa dadi ba. Nan da nan sai cece-kuce.

 

Magana ta gaskiya ita ce. Tun lokacin da aka tsayar da Bola Ahmed Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa na jamiyyar APC ya yi kamfen kuma an bashi goyon baya ya dauki niyyar zai aiwatar da salon Mulki ta fuskar tattalin arziki da siyasa irin yadda ya yi a zamanin da ya mulki jihar Lagos. Don haka a ranar da aka rantsar da shi ya cire tallafin man fetir. A tsakanin kwana 30 kuma ya sakarwa Naira mara ta nemawa kanta daraja a tsakanin kudaden musaya na duniya. A cikin wata biyu kuma ranar 7 ga watan Yuli 2023 ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin shugaban kwamitin fasalin harkar kudi da gyara harajin Najeriya. A wannan lokacin ne kuma aka tabbatar da Zacceus Adedeji mai baiwa shugaban kasa shawara ta fuskar haraji daga bisani kuma aka tabbatar da shi a matsayin shugaban hukumar FIRS. Su biyun nan, daya dan Lagos daya dan Ogun, sune suka tsara yadda za a tafiyar da haraji a kasar nan, bisa umarnin shugaban kasa. Sun shafe watanni 15 su hada nan, su kulla can, jama’armu kuma suna kwance a gida ko kuma sun can wata sharholiya.

 

A cikin aikin da suka gabatar ne, wanda suka rika tsakuro kadan-kadan ana aiwatarwa, a tsakanin wata 17, daga karshe kuma suka gabatar da dokoki sinfi- sinfi- har guda hudu, suka mika wa shugaban kasa shi kuma ya aika wa majalisa. Da aka yi karatun farko, sai shugaban kasa ya tafi Faransa tare da jamaarsa, yanzu kuma yana kasar Afirka da Kudu. A majalisar dattijai an yi karatun dokokin na biyu, wanda daga nan ne za a rabawa duk yan majalisar dattijai 109 kwafin wannan doka su koma su nazarceta. A wannan tsakanin ne ake sauraron masana, ake yin gyara, ake cirewa a saka sabo, ake muhawara a bainar jamaa.

Wannan shimfida ce

 

Bello Muhammad Sharada

At’tajdid News

You Might Also Like

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

2025 World Sight Day: NOA Advocates Eye Healthcare Consciousness 

ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI

The 2009 ASUU Agreement and the FGN’s Endless Broken Promises

Attajdid December 3, 2024 December 3, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Real Madrid ta amince da biyan Fam Miliyan 50 ga Dan wasa Dean Huijsen

Attajdid Attajdid May 15, 2025
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya aike da sakon ta’aziyya a kasar Ghana
An kashe ‘yan Nijeriya 1,172 da sace fiye da 1,000 a cikin wata tara – NHRC
Gwamnatin Tarayya, tare da haɗin gwiwar ƙasar Birtaniya, ta kaddamar da wani sabon shafin yanar gizo domin tallafa wa malamai a faɗin Najeriya.
IGP Deploys DIG To Oversee Security For Ondo Governorship   
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?