Yahudawan Sahyoniyya Sun Kai Jiran Hare-hare Sama da Ashirin (20) a Gaza
Rahotanni daga yankin Gaza sun tabbatarwa da At-tajdid News cewa an samu mutane da dama da suka rasa rayukansu da wasu da suka jikkata bayan harin da jiragen yaki na Isra’ila suka kai kan wani café mai suna “Twix”, da ke yammacin az-Zawaida, da ke tsakiyar Gaza.
Hukumomi a asibitin Shahidan Al-Aqsa sun tabbatar da karɓar gawarwaki da raunana masu yawa sakamakon harin da aka kai a rana ta yau.
A wani rahoto, tashar i24 ta rawaito daga wani jami’in tsaro na Isra’ila cewa sojojin saman Isra’ila sun kai hare-hare sama da ashirin (20) a cikin Gaza tun daga safiyar yau, suna mai cewa hare-haren na nufin tunkarar barazanar makamai daga ƙungiyoyin ’yan gwagwarmaya.
Daga cikin hare-haren, rahotanni sun tabbatar da shahadar mutum goma sha ɗaya (11) tare da raunuka da dama, a yankunan az-Zawaida, an-Nuseirat, da Jabalia.
A sansanin Al-Bureij, jiragen Isra’ila sun kai hari kan gidan iyalin Abdulhadi, inda aka samu hasarar rayuka da lalacewar dukiya.
A yankin ash-Shalayhat, kudu maso yammacin az-Zawaida, wani hari ya hallaka mutane da dama bayan bam ya fada kan wata tantar jama’a, inda mutane ke neman mafaka daga hare-haren baya-bayan nan.
A gefe guda, Kata’ib al-Qassam, ɓangaren soji na Hamas, ta fitar da sanarwa tana cewa:
“Muna nan kan yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma, kuma ba mu da wata alaka da abin da ke faruwa a yankin Rafah.”
Ƙungiyar ta bayyana cewa yankin Rafah yana karkashin ikon mamayar Isra’ila, kuma sadarwa da mayakanta da ke can ta katse tun watan Maris, lokacin da yaƙi ya sake ɓarke wa.
Ta ce ba ta da tabbacin ko mayakanta suna raye ko a’a.
A yankin Khan Younis kuma, jirgi maras matuki na Isra’ila ya kai hari a yankin Al-Mawasi, wanda ya janyo tsoro da fargaba a cikin jama’a.
Masu aikin gaggawa na ci gaba da neman mutanen da suka ɓace a yankunan da aka kai hari.
Wasu jami’an Amurka sun shaida wa kafafen yada labarai cewa gwamnatin Amurka ba za ta bari rikicin Gaza ya koma cikakken yaƙi ba, duk da cewa lamarin na ƙara yin muni a kowace rana.
Masu lura da al’amuran yankin na gargadi cewa yanayin jin kai a Gaza na kara tabarbarewa, yayin da asibitai suka cika, kuma kayan agaji su ke ƙarewa.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




