Babban Mufti Nazir Ayyad na kasar Masar ya ce tallafawa al’ummar kasar Falasdinu wani muhimmin aiki ne na addini da kuma kasa wanda bai kamata a yi watsi da su ba.
Ya yi kira ga cibiyoyi da gwamnatocin kasa da kasa da su kara kaimi ga ayyukan agaji ga al’ummar Palasdinu da kuma ba da agajin jin kai cikin gaggawa ba tare da tsangwama ba.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




