By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran.
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran.
International News

Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran.

Attajdid
Last updated: 2025/06/17 at 10:57 AM
Attajdid Published June 17, 2025
Share
SHARE

Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran.

Tue, 17 Jun 2025 10:17:39 GMT+0100

Matatar man ƙasar Isra’ila dake yankin Haifa ta dakatar da ayyukanta gaba daya bayan hari da Iran ta kai mata.

Hukumar gudanarwar matatar man ƙasar Isra’ila dake yankin Haifa ta sanar da cewa matatar ta dakatar da ayyukanta ɗungurungum bayan harin da Iran ta kai mata.

Kamfanin Bazan Group dake kula da matatar ya ce harin na Iran ya tilasta musu tsayar da gaba ɗaya — a yayin da sabon rikicin na yankin Gabas ta Tsakiya ke ɗaukar zafi tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna yi wa juna kallon hadarin kaji.

Bazan Group ya bayyana cewa, harin rokokin Iran ya lalata tashar wutar lantarki da matatar ke amfani da shi.

Harin na Iran ya kuma halaka ma’aikata uku a matatar ta Haifa, kamar yadda hukumomin Isra’ila suka sanar.

Wannan na faruwa a ci gaban hare-haren ramuwar gayya da makamai masu linzami da Iran ke kaiwa, bayan jiragen Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare da kawo yanzu suka yi ajalin mutane sama da 220 a sassan Iran, har da Tehran, Babban birnin ƙasar.

Kashi 70 na mutanen da Isra’ila ta kashe a Iran mata da ƙananan yara ne; da wasu manyan jami’an tsaro da wani masanin kimiyyar makamashin nukiliya.

Majiyar mu ta ruwaito Isra’ila na cewa ta ƙaddamar da hare-haren ne domin daƙile Iran, wadda ke dab da mallakar makamin nukiliya a cikin wannan shekara, ko cikin watanni kaɗan masu zuwa.

Ana iya tuna cewa Firaiminista Banjamin Netanyahu ya bayyana cewa hallaka shugaban addinin Iran, Ayatullah Khamene’i zai yi tasiri wajen kawo karshen rikicin.

A nata bangaren Iran ta bayyana cewa Isra’ila za ta yabawa aya zaƙinta, kan waɗannan hare-haren ragoncin da ta kai wa fararen hula da cibiyoyin soji da tashoshin makamashin nukiliyarta.

Ta kuma bayyana harin bai tsayar da shirinta na nukiliya domin samar da wutar lantarki da sauran abubuwa na zaman lafiya ba.

Ramuwar gayyar Iran ta shafi cibiyoyin sojin Isra’ila da tashar wutar lantarki da matatar mai, baya ga halaka mutane sama da 24 da lalata gine-gine a wurare daban-daban, ciki har da birnin Kudus, da kuma Tel Aviv, babban birnin ƙasar Isra’ila.

Mai rahoto
Mustapha Garba Usman

 

At’tajdid News

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid June 17, 2025 June 17, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Group Hails Filling Professor, PhDs As Candidates For LG Chairman In Jigawa

Attajdid Attajdid August 26, 2024
Hezbollah ta tabbatar da kisan shugabanta Hassan Nasralla
An Kaiwa Jagororin Kungiyar Hamas Hari a Doha
Iran na binciken ɓatan wasu ƴan Indiya uku a cikin ƙasarta
Gov. Umar Namadi: Taking Jigawa to greater heights.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?