Iran na binciken ɓatan wasu ƴan Indiya uku a cikin ƙasarta
Ofishin Jakadancin Iran da ke Indiya ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan batun ɓatan wasu ‘yan asalin Indiya guda uku da suka ɓace a birnin Tehran tun farkon wannan watan.
Mutanen, dukkansu daga jihar Punjab da ke arewacin Indiya, sun fara ya da zango a Iran a ranar 1 ga Mayu, kafin su ƙarasa Australia, inda aka yi musu alkawarin samun ayyuka da albashi masu tsoka.
Iyayensu da danginsu sun yi zargin cewa an yi garkuwa da su ne tun isowarsu Iran, kuma suna bukatar fansa har na rupees miliyan biyar (kimanin dala 63,000 ko fam 47,000).
A ranar Alhamis, ofishin jakadancin Iran ya wallafa a shafin X cewa zai dinga sanar da hukumomin Indiya duk wani cigaba da ake samu a binciken tare da yin gargadi kan haɗarin bin haramtattun hanyoyi wajen shiga ci-rani
Wannan sanarwar ta zo ne kwana guda bayan da ofishin jakadancin Indiya a Iran ya ce ya “ɗauki wannan al’amarin da muhimmanci” tare da buƙatar a gaggauta gano inda ‘yan Indiyan suke da tabbatar da lafiyarsu.
Da dama daga cikin ‘yan Indiya, musamman daga jihar Punjab, na yawan yin ƙaura zuwa ƙasashe masu da suka ci gaba domin neman aiki da rayuwa mafi inganci.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




