Shugaban Hezbollah na Labanon ya ce abin da ya faru a Labanon a ranar Talata da Laraba za a iya daukar sa a matsayin “ayyana yaki”.
“Da wannan farmakin, makiya sun ketare dukkan… jan layi,” in ji Hassan Nasrallah a fitowarsa ta farko a talabijin bayan kai hare-haren, yana zargin hakan da kokarin “kashe mutane a kalla 5,000” a cikin “babbar takalar ƙungiyar da ba a taɓa ganin irin ta ba.
Ministan lafiya na Labanon Firass Abiad ya ce mutum 37 ne suka mutu sannan wasu fiye da 3,500 suka samu raunuka a wani sabon adadin da aka samu, bayan da aka tayar da na’urorin sadarwa na ‘yan kungiyar Hizbullah a fadin kasar ta Lebanon, a hare-haren da ake zargin Isra’ila ke da hannu.
Abiad ya ce an kashe mutum 25 a ranar Laraba da kuma 12 a ranar Talata, wanda ya bayyana adadin wadanda suka mutu gaba daya ya kai 32.
Daga basani Isra’ila ta ba da rahoton sake harba makaman roka daga Lebanon guda 10 inda suka sauka a yankunan da ke Upper Galilee da ke arewacin Isra’ila, kamar yadda
tashar talabijin ta Channel 12 ta Isra’ila ta ce an lalata “gine-gine” a cikin “yankunan Yahudawa ‘yan kama wuri zauna na Zar’it” sakamakon fadowar rokoki daga Lebanon ta kara da cewa ba a samu rahoton jikkata ba.
A wani rahoto daga majiyarmu ta yankin gabas ta tsakiya ministan harkokin wajen Italiya Antonio Tajani ya bayyana cewa, zai tattauna yiwuwar samar da sabbin tsare-tsare na zaman lafiya a Zirin Gaza da wasu kasashen Yammacin Duniya biyar da aka fi sani da kungiyar Quint.
Quint ƙungiyar yanke shawara ce ta yau da kullum wacce ta ƙunshi Amurka, Burtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya. “Muna cikin damuwa game da halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya da tattaunawa da su domin samun yiwa tsagaita wuta a yankin Gaza.
“Muna ci gaba da aiki tare don samar da zaman lafiya, tsagaita bude wuta, da kuma sako mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji shi.
Zuwa yanzu yaƙin Isra’ila a Gaza ya shiga rana ta 350, inda ta kashe kusan Falasɗinawa 41,272 yawacinsu mata da yara tare da jikkata kusan 95,551 kuma wani ƙiyasi ya nuna cewa fiye da mutum 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa.
At-tajdid News.




