Gwamnatin Sokoto ta bayar da kwangilar sake gina madatsar ruwa ta Lugu
Gwamnatin jihar Sokoto ta amince da kwangilar sake gina madatasar ruwan ta Lugu da ke ƙaramar hukumar Wurno a jihar, wadda za ta laƙume naira biliyan 32.4.
Gwamnan jihar Ahmed Aliyu wanda ya sanya wa kwangilar hannu, ya bayyana cewa madatsar za ta yi matuƙar taimakawa wajen bunƙasa fannin noman rani idan aka kammala ta, bayan da ta rufta a shekarar 2010.
“Wannan gagarumin aikin ba yana nufin sake gina madatsar ruwan kawai ba – har ma muna sake dawo da wata muhimmiyar fata, da inganta rayuwa tare da bunƙasa ɓangarorin tattalin arziƙi da ke neman tallafi tsawon shekaru,” in ji gwamnan.
Gwamnatin Sokoto ta ɗauko aikin sake gina madatasar ruwan ne tare da haɗin gwiwar Bankin Duniya, kuma aikin zai haɗa da sake gina bangwayen madatsar masu faɗin kilomita 7.1 da sake gina hanyoyin mota da suka haɗa muhimman wuraren da ake noman rani a Wurno, da farfaɗo da filayen noman ranin masu faɗin kadada 1,200 da kuma samar da ma’ajiyar ruwa mai ɗaukar ruwa cubic miliyan 64 da sauran su.
Madatasar ruwan ta Lugu dai na da muhimmanci a ɓangarorin noma da kiyon kifi da samar da ruwan sha da aikin yi ga al’ummar yankunan.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




