Rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe sojojinta uku a wani fada da aka gwabza a arewacin Gaza yayin da take ci gaba da kai wani gagarumin farmaki a yankin.
Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce sojojin sun “fadi mutu ne a lokacin da ake gwabza fada a arewacin Gaza”, wanda ya kawo adadin sojojin Isra’ila da aka kashe a yakin Gaza zuwa 361 tun bayan fara kai farmakin kasa a yankin a bara.
Akalla Falasdinawa 9 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wasu fararen hula a yammacin birnin Gaza.
Wata majiyar lafiya daga asibitin al-Ahli Arab ta shaida wa Anadolu cewa an kai wadanda suka jikkata da dama cibiyar lafiyar da kuma gawarwakin mutane tara bayan harin saman.
An kai harin ne a sansanin ‘yan gudun hijira na Shati, kamar yadda shaidu suka shaida wa Anadolu.
Yaƙin da Isra’ila take yi a Gaza, wanda ya shiga kwana na 385, ya kashe Falasɗinawa aƙalla 42,847 da jikkata fiye da 100,000, kan ana ƙiyasi mutum fiye da 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzai.
At-tajdid News.




