By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Tsohon Shugaba Sudan Umar Al-Bashir Yana Fuskantar Tuhoma Daga (ICC) Duk Da Yana Fama Da Rashin Lafiya
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Tsohon Shugaba Sudan Umar Al-Bashir Yana Fuskantar Tuhoma Daga (ICC) Duk Da Yana Fama Da Rashin Lafiya
International News

Tsohon Shugaba Sudan Umar Al-Bashir Yana Fuskantar Tuhoma Daga (ICC) Duk Da Yana Fama Da Rashin Lafiya

Attajdid
Last updated: 2024/09/25 at 3:10 AM
Attajdid Published September 25, 2024
Share
SHARE

An dauke tsohon shugaban Sudan Omar al-Bashir daga babban birnin kasar Sudan da yaki ya daidaita zuwa garin Merowe da ke arewacin kasar domin kula da lafiyarsa, kamar yadda lauyansa ya bayyana.

Lauya na sa Mohamed Hassan al-Amin ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an kai tsohon shugaban mai shekaru 80 wani wurin da ake tsare da shi a Merowe kafin a yi masa magani a wani asibiti a garin.

“Yana bukatar a duba lafiyarsa da kuma duba lafiyarsa lokaci-lokaci.

Wani lokaci yana samun wasu matsaloli, wanda ke bukatar bin diddigi. Amma yanayin da yake ciki ba mai tsanani ba ne a yanzu,” in ji Amin.

Ya kara da cewa, har yanzu ba a gano abin da ke damunsa ba, kuma za su iya bukatar magani a wata kasa a wajen Sudan, yana mai cewa wannan shi ne karon farko da aka dauke Bashir daga babban birnin kasar.

Ana tuhumar Al Bashir da laifin cin hanci da rashawa da almundahana da kudade ba bisa ka’ida ba, sannan kuma ya fuskanci wasu shari’o’in kafin yaki ya barke a watan Afrilun 2023.

An tsare shi a baya-bayan nan a wani sansanin soji da ke Omdurman, wani yanki na babban birnin kasar Sudan inda sojojin suka ja tunga a yakin da suke yi da dakarun Rapid Support Forces (RSF).

An gabza kazamin fada a Omdurman, kuma RSF ta yi ruwan bama-bamai a unguwannin birnin ranar Talata, in ji wasu shaidu na gani da ido.

Duk da halin da yake kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Kasa da Kasa (ICC) na neman Al Bashir bisa zargin aikata laifukan yaki da laifukan cin zarafin bil adama da kuma kisan kare dangi da suka shafi rikicin da ya barke a Darfur daga shekara ta 2003 duk da irin wannan karfi da (ICC) take da shi duniya ta kasa daukan mataki akan Isra’ila duba  irin yadda suke kisan kare-dangi a Gaza.

Shi ma wani tsohon minista Abdelrahim Mohamed Hussein da ke fuskantar sammacin ICC, an mika shi kai shi Merowe tare da Bashir don kula da lafiyarsa, a cewar Amin.

Haka shi ma wani tsohon babban jami’i, Bakri Hassan Saleh, daya daga cikin makusantan Bashir a tsawon shekaru talatin da ya yi yana mulki, tuni aka kai shi asibitin Merowe.

TRT Afarka Hausa.

At-tajdid News.

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid September 25, 2024 September 25, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Netanyahu ya yi Barazanar Lalata Lebanon Saboda Hezbollah

Attajdid Attajdid October 9, 2024
The Gaza death toll has risen to more than 40,098 Palestinians amid Israel’s continued bombardment of the besieged enclave since October 7, says the health ministry.
More than 900 Hajj pilgrims die in Saudi Arabia over excessive heat
Kungiyar Hamas Tana Kira Ga Mutanan Duniya da su Fito Zanga-zanga Dakatar da Kisan Kiyashi da Yunwa a Gaza
Isra’ila Ta Cigaba Da Ruwa Bama-bamai Kan Fararen hula A Gaza
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?