By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: An Kashe Jagoran ’Yan Bindigar Kaduna a Rikicin ’Yan Fashin Daji
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > An Kashe Jagoran ’Yan Bindigar Kaduna a Rikicin ’Yan Fashin Daji
News

An Kashe Jagoran ’Yan Bindigar Kaduna a Rikicin ’Yan Fashin Daji

Attajdid
Last updated: 2024/09/23 at 8:48 PM
Attajdid Published September 23, 2024
Share
SHARE

Wani fitaccen jagoran ’yan bindiga a Jihar Kaduna, Kachalla Tukur Sharme, ya gamu da ajalinsa a rikicin da ya barke tsakanin kungiyoyin ’yan ta’adda masu gaba da juna.

Kachalla Tukur Sharme shi ne wanda ya jagranci sace dalibai 121 daga makarantar sakandare ta Bethel Baptist da ke Kujama a ranar 5 ga Yuli, 2021.

Shi da yaransa da dama sun sheka lahira ne a wani ƙazamin fada tsakaninsu da abokan gabansu ’yan bindiga a Dajin Rijana da ke Jihar Kaduna, a cewar kwamishinan tsaro, Samuwal Aruwan, a ranar Litinin.

Kwamishin ya ce an kashe ’yan bindiga biyu daya bangaren, a musayar wutar wadda majiyoyin leken asiri suka ruwaito cewa ’yan bindiga biyar sun jikkata, kuma a halin yanzu suna buya a yankin, inda suke neman agajin jinyar raunukan da suka samu.

“Sharme, wani dan bindiga da ya garkuwa da daruruwan mutane, ya kuma yi awon gaba da shanun da ba za su kirgu ba, amma ya gamu da ajalinsa a yakin da aka yi tsakanin kungiyarsa da wasu ’yan fashin daji.

“Rikicin ya faru ne a karshen mako a wani wuri da ake kira ‘Hambakko’, a cikin Dajin Rijana da Kaso, wanda ya hada da Kachia da wasu sassan kananan hukumomin Chikun da Kajuru,” inji shi.

Aruwan ya kara da cewa, Sharme ya sha guje wa jami’an tsaro da kyar, kuma ana nemansa ruwa a jallo kafin a harbe shi har lahira.

Kwamishinan ya kara da cewa, Sharme da yaransa ne ke da alhakin kai hare-hare, kashe-kashe, da kuma garkuwa da mutane a yankunan Millennium City, Maraban Rido, Kujama, Kajuru, Maro, da kauyukan da ke yankin Kateri, da kuma wasu kananan hukumomin Kagarko, Kachia da Birnin Gwari.

Har ila yau ayyukan ta’addancin da ya aikata sun tsallaka har zuwa jihohin Katsina da Nijar da ke makwabtaka da Kaduna, wadanda su ma suke fama da ta’addanci.

Ya bayyana cewa daya daga cikin munanan ayyukan da Kachalla Sharme akwai sace dalibai 121 daga makarantar sakandare ta Bethel Baptist da ke Kujama a ranar 5 ga Yuli, 2021.

Ya kuma gargadi mazauna garuruwan Rijana, Kaso, Kasarami, Jaka da-Rabi, Kajuru, da kuma Dutse da kada su taimaka wa duk wani mutum da ke dauke da raunin harbin bindiga.

Ya bukace su da su tuntubi jami’an tsaro mafi kusa ko kuma su isa dakin aikin tsaro na jihar Kaduna.

Mai rahoto;
Salihu Garba.

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid September 23, 2024 September 23, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Da Yuwar Hizbullah Zasu Maida Martani ga Isra’ila

Attajdid Attajdid August 26, 2024
Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900
Gunman Crossing From Jordan Kills Three Israelis at Border
IRAN EXECUTED ISRAEL CONVICTED SPY
Za mu kare masu zanga-zangar tsadar rayuwa matuƙar ta lumana ce – ‘Yan Sandan Najeriya.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?