Kamar yadda Jaridar Hausa Daily Post kawoGwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa, ta bayyana zunzurutun kuɗi har sama da kimanin Naira Biliyan 30 a matsayin adadin da ta kashe a cikin shekara ɗaya da watanni uku kan ƙalubalen tsaro da wasu sassan jihar ke fuskanta.
Duk da hakan bai kawo karshin barayin dajiba a wasu sassa na Jahar.Jaridar Hausa Daily Post ta ruwaito cewa, kwamishinan tsaro da harakokin cikin gida na gwamnatin jihar, Nasiru Mu’azu Ɗanmusa ne ya bayyana hakan, a wurin wani taro da gwamnatin jihar ta shirya a shiyyar Funtua domin ganawa da al’ummar yankin kan yadda gwamnatin ta tsara kasafin kuɗi na shekarar 2024.
Inda a cikin jawabinsa, Nasiru Ɗanmusa ya yi bayani kan yadda gwamnatin Dikko Raɗɗa ta riski halin da sha’anin tsaro ke ciki ranar 29 ga watan Mayun 2023 zuwa yanzu.
Ya bayyana Nasarorin da gwamnatin ta samu a yayin da take fafutika domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma ƙara da cewa, “a kowane wata gwamnatin jihar na ware Naira Miliyan Uku ga shugabannin ƙananan hukumomin da matsalar tsaro ta shafa domin siyan man fetur ɗin da za su yi sintiri.
“Nasir Ɗanmusa, ya kuma jaddada cewa gwamnatin jihar a shirye take da ta karɓi koken duk wata karamar hukumar dake fuskantar ƙalubalen tsaro domin basu kuɗaɗen da za su magance wata matsala ta tsaro dake addabar su.
At-tajdid News.




