A yau ne aka wayi gari da wani mumunan hari na makami mai linzami da yahudawan sahyoniyya su kai kan sahun masu ibada a lokacin sallar asubahi a makarantar Al-Tabaeen da ke unguwar Al-Daraj, lamarin da ya yi sanadin shahidar fiye da mutane 100 tare da jikkata wasu mutane da dama.

Matsayar Hamas: Ta bayyana hakan a matsayin “Kisan kiyashin da aka yi a makarantar Al-Taba’een a matsayin babban laifi ne da yake kara ta’azzara a cikin jerin laifukan da ‘yan Nazi suka aikatawa a Gaza” ta kara da cewa “Kisan kiyashin da aka yi a makarantar tabbatacce ne karara ya farune daga gwamnatin yahudawan sahyoniya da kuma ci gaba da yakin da suke yi da al’ummar Palastinu” “Sojojin mamaya suna haifar da munanan kalamai wanda ba na gaskiyaba ga fararen hula da makarantu da kuma asibitoci.
“Hamas ta tabbatar da cewa karuwar laifukan yahudawan sahyoniya a zirin Gaza ba za su ci gaba ba idan ba tare da goyon bayan Amurka ba, wanda ya sa Washington ta zama abokiya a cikinta.
“Ma’aikatar Harkokin Wajen Masar ta ce Kisan Falasdinawa da gangan, wata kwakkwarar shaida ce ta rashin san kawo karshen yakin da Isra’ila take kawa a Gaza.Ma’aikatar Harkokin Wajen Jordan tayi Allah wadai da kakkausar harshe akan harin bam da Isra’ila ta kai a makarantar Al-Tabaeen, wanda ke dauke da mutanen da suka rasa rayukansu da matsugunansu a unguwar Al-Daraj da ke zirin Gaza.Ma’aikatar tsaron farar hula a Zirin Gaza ta kara da cewa an kai harin kan benaye biyu na makarantar, na farko da aka yi wa mata gidaje, kuma na kasan dakin taron addu’o’i ne ga ‘yan gudun hijirar.
An kai hari kan cibiyoyi 13 da ake tsugunar da ‘yan gudun hijirar tun farkon wannan wata. Muna kira ga duniya da ta sa baki cikin gaggawa don dakatar da kisan kiyashin da ake yi wa fararen hula marasa tsaro a matsuguninsu.
Mai rahoto;
Musa Badamasi Gama.
At-tajdid News.




