By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Belgium ta bi sahun ƙasashe sama da 140 da suka amince da cin gashin kan Falasɗinu
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Belgium ta bi sahun ƙasashe sama da 140 da suka amince da cin gashin kan Falasɗinu
International News

Belgium ta bi sahun ƙasashe sama da 140 da suka amince da cin gashin kan Falasɗinu

Attajdid
Last updated: 2025/09/05 at 4:31 PM
Attajdid Published September 5, 2025
Share
SHARE

Zuwa yanzu ƙasashe 147 ne suka amince da ayyana Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta, bayan da Belgium a yau Talata ta kawo ƙarshen doguwar muhawarar da take tafkawa a zauren majalisarta kan wannan ƙudiri tare da amincewa da shirin amincewa da halascin yankin a matsayin cikakkiyar ƙasa.

 

Yayin zaman babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya da zai gudana a watan nan ne Belgium, za ta bayyna amincewa da halascin yankin na Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta, kamar yadda Maxine Prevot, mataimakin Firaministan ƙasar ta Turai ke bayyanawa a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X yau Talata.

 

Prevot ya bayyana cewa baya ga amincewa da halascin ƙasar Falasɗinu, ƙasar za kuma ta lafta takunkumai har guda 12 kan gwamnatin Isra’ila baya ga haramta shigo mata da kayan da aka sarrafa a yankin Yahudawa ƴan kama waje zauna da ke yammacin gaɓar kogin Jordan.

 

Prevot wanda mamba ne a jam’iyyar masu tsaka-tsakan ra’ayi ta Centrist Le Zangaj ‘Les Engages’, ya ce Belgium ta ɗauki wannan mataki ne la’akari da halin ƙuncin da Isra’ila ta jefa Falasɗinawa musamman a yankin Gaza, sai dai ya ce amincewa da halascin zai fara aiki a hukumance ne bayan Hamas ta saki ilahirin fursunonin da ke hannunta, haka zalika sai ƙungiyar ta janye daga jagorancin Gaza.

 

 

Tuni ma’aikatar harkokin wajen Falasɗinu ta yi maraba da matakin tare da kira ga sauran ƙasashe su bi sahu don amincewa da halascin yankin a matsayin ƙasa.

 

Kawo yanzu ƙasashe 147 ne suka amince za su ayyana yankin na Falasɗinu a matsayin halastacciya, adadi mafi yawa da aka taɓa samu a tarihi tun bayan kafuwar Isra’ila a tsakar yankin da ke ƙarƙashin ikon Birtaniya a lokacin mulkin mallaka.

 

Wannan adadi na ƙasashe shi ke wakiltar kashi 75 na zaman taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya, zaman da ake saran ya mayar da hankali kan halin da ake ciki a Gaza da sauran rikice-rikicen da duniya ke fama da su.

 

Daga: Muhammad Zangina Kura

 

At’tajdid News

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid September 5, 2025 September 5, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

SHIRIN TRUMP KAA MAKOMAR: GAZA!.

Attajdid Attajdid September 1, 2025
Majalisar Dattawa ta Amince Tinubu ya Ciyo bashin $2.2bn
An Yi Jana’izar Baturkiyya-Ba’amurkiya ‘Yar Gwagwarmaya Da Aka Kashe a Gabar Yammacin Kogin Jodan
Poll:: Governor Namadi Receives Hundreds Of Decamped From PDP AND NNPP
Sojojin Isra’ila Suna Fuskantar Barazana Mai Tsanani a Yakin da Suke yi a Gabas ta Tsakiya
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?