Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Isra’ila ta taɓa kasancewa mafi ƙarfi wajen matsa lamba a majalisar dokokin Amurka, amma yanzu ta rasa wannan ƙarfi.
Ya ce ba wanda ya yi wa Isra’ila irin taimakon da ya yi mata, ciki har da hare-haren baya-bayan nan akan Iran. Trump ya ƙara da cewa dole Isra’ila ta kawo ƙarshen wannan yaƙi domin yana cutar da ita, inda ya nuna cewa duk da ta ci gaba da yaƙi, tana rasa tasiri a fagen hulɗar jama’a musamman a majalisar dokoki.
Ministan harkokin waje na Belgium ya bayyana cewa ƙasarsa za ta amince da matsayin Falasɗinu a zaman Majalisar Ɗinkin Duniya. Haka kuma Belgium za ta kafa takunkumi mai tsauri kan gwamnatin Isra’ila, tare da ɗaukar matakin yin zabe a taron Turai domin dakatar da haɗin gwiwa da Isra’ila.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At’tajdid News




