By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Gina Jamiyya Ne A Gabanmu Ba Zaɓar Wanda Zai Yi Takarar Ba – ADC
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Gina Jamiyya Ne A Gabanmu Ba Zaɓar Wanda Zai Yi Takarar Ba – ADC
News

Gina Jamiyya Ne A Gabanmu Ba Zaɓar Wanda Zai Yi Takarar Ba – ADC

Attajdid
Last updated: 2025/07/28 at 9:45 AM
Attajdid Published July 28, 2025
Share
SHARE

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana cewa har yanzu lokaci bai yi ba da za ta yanke hukunci kan wanda zai zama ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaben 2027.

Bolaji Abdullahi, mukaddashin Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a Abuja a ranar Asabar 26 ga Yuli, inda ya ce jam’iyyar ta mayar da hankali kan gina ingantacciyar jam’iyya mai ƙarfin tasiri a halin yanzu.

Ya ce: “Ba mu da wani ɗan takara da muke fifitawa a yanzu. Babu wata tattaunawa da ake yi a halin yanzu kan wanda zai zama ɗan takarar jam’iyya.

“Babu wanda ya taɓa kawo wannan batu a jam’iyyar. Muna ganin cewa har yanzu lokaci bai yi ba. Abin da muke mayar da hankali a kai yanzu shi ne gina jam’iyya mai ƙarfi da za ta iya cimma manufofin da muka sa a gaba.”

A halin yanzu, ana rade-radin cewa wasu fitattun ‘yan siyasa uku na sha’awar tikitin shugaban ƙasa a jam’iyyar ta ADC. Wadanda su ka haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi; da kuma tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi.

Sai dai har yanzu ba ɗaya daga cikinsu ba ya fito fili ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar karkashin ADC.

Mai rahoto;
Salihu Garba.

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid July 28, 2025 July 28, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Abin da ya Kamata ku Sani Kan ƙungiyar da Putin ke Karɓar Baƙuncinta: BRICS

Attajdid Attajdid October 25, 2024
Ukraine Says Russian Attacks Injure at Least 5, Cause Fires
Ana Kyamar Musulmai a Kasashan Turai Sabo da Yakin da Ake yi Yankin Gabas-ta-tsakiya 
AMBALIYAR RUWA A GARIN MAIDUGURI
Ex-president Buhari Donates N10 million To Victims Of Jigawa Tanker Explosion 
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?