Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana cewa har yanzu lokaci bai yi ba da za ta yanke hukunci kan wanda zai zama ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaben 2027.
Bolaji Abdullahi, mukaddashin Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a Abuja a ranar Asabar 26 ga Yuli, inda ya ce jam’iyyar ta mayar da hankali kan gina ingantacciyar jam’iyya mai ƙarfin tasiri a halin yanzu.
Ya ce: “Ba mu da wani ɗan takara da muke fifitawa a yanzu. Babu wata tattaunawa da ake yi a halin yanzu kan wanda zai zama ɗan takarar jam’iyya.
“Babu wanda ya taɓa kawo wannan batu a jam’iyyar. Muna ganin cewa har yanzu lokaci bai yi ba. Abin da muke mayar da hankali a kai yanzu shi ne gina jam’iyya mai ƙarfi da za ta iya cimma manufofin da muka sa a gaba.”
A halin yanzu, ana rade-radin cewa wasu fitattun ‘yan siyasa uku na sha’awar tikitin shugaban ƙasa a jam’iyyar ta ADC. Wadanda su ka haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi; da kuma tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi.
Sai dai har yanzu ba ɗaya daga cikinsu ba ya fito fili ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar karkashin ADC.
Mai rahoto;
Salihu Garba.
At-tajdid News.




