Burkina Faso da Senegal za su ƙulla alaƙar tsaro
Shugaban gwamnatin mulkin soji na ƙasar Burkina Faso, Ibrahim Traore ya gana da Firaministan Senegal, Ousmane Sonko domin tattauna hanyoyin haɗin gwiwa domin yaƙi da rashin tsaro da sauran abubuwan da suka shafi ƙasashen biyu.
An gudanar da tattaunawar ce a ranar 16 ga watan Mayu a babban birnin Burkina Faso, Ouagadougou, kamar yadda kafar Burkina24 mai zaman kanta a ƙasar ta ruwaito.
“Na zo ne domin nuna goyon baya ga Shugaban Ƙasa Traore da gwamnatinsa da ma mutanen ƙasar a ƙoƙarin da suke yi na yaƙi da ta’addanci da aka ƙaƙaba musu, sannan mu duba hanyoyin da za mu ƙulla alaƙa da haɗin gwiwar taimakon juna,” in ji Sonko bayan tattaunawar.
Firaministan ya ce rashin tsaron ba zai tsaya a Burkina Faso da Mali da Nijar kaɗai bam “babu ƙasar da za ta tsira idan ta’addancin ya cigaba da faɗaɗa a yankin Afirka ta Yamma,” in ji shi.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu




