By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Adadin Waɗanda Isra’ila ta Kashe a Gaza ya Kusan kai 47,200, an Gano ƙarin Gawawwaki 53
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Adadin Waɗanda Isra’ila ta Kashe a Gaza ya Kusan kai 47,200, an Gano ƙarin Gawawwaki 53
International News

Adadin Waɗanda Isra’ila ta Kashe a Gaza ya Kusan kai 47,200, an Gano ƙarin Gawawwaki 53

Attajdid
Last updated: 2025/01/23 at 6:57 AM
Attajdid Published January 23, 2025
Share
SHARE

Likitocin Falasdinawa sun gano gawawwakin Falasdinawa 53 daga karkashin baraguzan gine-gine a Gaza, lamarin da ya kawo adadin wadanda suka mutu sakamakon yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a yankin tun daga watan Oktoban 2023 zuwa 47,161, in ji ma’aikatar lafiya.

 

Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, an kuma kwantar da mutane 19 da suka jikkata a asibitoci cikin sa’o’i 24 da suka gabata, wanda ya kawo adadin wadanda suka jikkata zuwa 111,166 a harin da Isra’ila ta kai.

 

“Mutane da yawa har yanzu suna makale a karkashin baraguzan gine-gine da kuma kan tituna yayin da masu ceto ba su iya isa gare su,” in ji ta.

 

Sojojin Isra’ila sun kashe wani Bafalasɗine magidanci a gaban matarsa da ‘ya’yansa uku yayin da yake tuƙa mota a birnin Jenin citda ke arewacin Gaɓar Yamma da Kogin Jordan a yayin da Isra’ila ke ci gaba da kutsawa yankin.

 

Wani bidiyo da iyalan mutumin suka ɗauka wanda aka riƙa watsawa a shafukan intanet ya nuna mawuyacin halin da Ahmed Nimer Obeidi Shayeb lokacin da aka harbe shi.

 

A yayin da yake tattaunawa da Anadolu Agency, Bashir Matahen, Daraktan Watsa Labarai na Birnin Jenin, ya ce Ahmed Shayeb yana tare da iyalansa matarsa da ‘ya’ya uku suna hanyar komawa gida yayin da wani sojan Isra’ila gwanin harbi daga ɓoye ya buɗe masa wuta.

 

A gefe guda, Matahen ya ce Falasɗinawa fiye da 600 sun tsere daga sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin a yayin da dakarun Isra’ila suke ci gaba da kutsawa birnin na Jenin.

 

Isra’ila ta ƙaddamar da jerin hare-hare a birnin Jenin na Gaɓar Yammacin Kogin Jordan inda ta kashe Falasɗinawa aƙalla tara da jikkata aƙalla mutum 40, in ji jami’in kiwon lafiyar Falasɗinu, a daidai lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta ƙulla da Hamas ta shiga kwana na huɗu a Gaza.

 

A Tel Aviv, an jikkata mutum huɗu a wani hari da aka kai musu da wuƙa ko da yake jami’an tsaro sun kashe mutumin da ya kai harin, a cewar ‘yan sandan Isra’ila.

 

Hukumomi sun ce mutumin da ya kai harin “ɗan ƙasar waje” kuma yana da shekaru 28 suna masu cewa harin na ta’addanci ne. TRT African Hausa.

 

 

Mai rahoto;

M.B.S.Gama.

 

 

At-tajdid News

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid January 23, 2025 January 23, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Jigawa To Award N1.2 Billion Contract For Solar Powered Street Light

Attajdid Attajdid November 28, 2024
Mayaƙan Hezbollah sun harba rokoki da dama a yankin Tel Aviv, babban birnin Isra’ila inda suka sauka a kusa da wani babban kanti a garin Ramat Gan ranar Litinin. Rahotanni sun ce lamarin da haddasa mummunar gobara a gine-gine tare da jikkata aƙalla mutum biyar,
DAKARUN MAMAYA NA ISRA’IL SUN CI GABA DA MUZGUNAWA MAZAUNA GAZA.
Hare-hare Suna Kara Zafafa Tsakanin Dakarun Mukawama ”yan Kasa da Yahudawan Sahyoniyawan ‘Yan Kama Wuri Zauna a Gaza
Birtaniya, Australia da Canada sun amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa gabanin babban taron MDD
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?