By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: GOMNATIN KANO ZATA FARA YIWA BAKI RIJISTAR ZAMA
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > GOMNATIN KANO ZATA FARA YIWA BAKI RIJISTAR ZAMA
News

GOMNATIN KANO ZATA FARA YIWA BAKI RIJISTAR ZAMA

Attajdid
Last updated: 2024/11/05 at 5:18 AM
Attajdid Published November 5, 2024
Share
SHARE

Gwamnatin jihar Kano ta da ke arewa maso yammacin Najeriya ta kafa wani kwamitin ƙwararru da zai yi aikin yiwa baƙi ƴan ƙasashen waje mazauna birnin rijista musamman waɗanda suke gudanar da kasuwanci.

 

Gwamnati ta ce ta ɗauki matakin ne domin samun alƙaluman mutanen da suka fito daga ƙasashen ƙetare kuma suke gudanar da harkokin kasuwanci a jihar, ta yadda za a haɓɓaka kudin shiga da kuma tsaro da samar da ayyukan yi.

 

Kwamitin wanda ke ƙarƙashin ofishin sakataren gwamnatin Kano, zai tattara bayanan baƙi ƴan ƙasashen waje da ke aiki walau na kamfani ko a wata ma’aikata ko kuma kasuwanci.

 

Shugaban kwamitin, Lawan Isa Kibiya ya ce aikin da za su yi zai taimaka wajen tabbatar da ganin baƙin waɗanda mafi yawa ƴan kasuwa ne su na biyan haraji kamar yadda doka ta yi tanadi.

 

 

Ya ƙara da cewa hakan zai bai wa gwamnati ƙwarin gwiwar ‘‘ƙoƙarin ganin ta samar da yadda za ta ba su kariya ta fuskar tsaro’’

 

Kwamishinan ma’aikatar ciniki ta jihar Kano, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya wanda manba ne a kwamtin ya ce ‘‘aikin bai taƙaita ga buƙatar tattara haraji kaɗai ba, duk duniya akwai ƙa’idoji da aka kafa a doka, waɗanda idan baƙo ya je zai yi kasuwanci ga ƙa’idojin da ya kamata ya bi, sannan su ma ƴan gari ga ƙa’idojin da ya kamata su bi.’’

 

Ya ƙara da cewa ‘‘idan ka shiga wannan manyan kasuwannin namu, musamman kantin kwari, za ka ga baƙin su ne mafi yawa ke ƙerawa, su yi packaging su kuma yi kasuwanci kai tsaye.’’

 

Adamu Kibiya, ya kara da cewa ire-iren waɗannan abubuwan gwamnati ta kalla shi yasa ake ƙoƙarin fito da tsarin da zai taimaki al’umma musamman wajen samar da ayyuka da kare martabar kasuwanci: ‘‘Idan muka zura ido mu ka yi gaba to zai zamo nan gaba mun koma maula, mutanen mu sun koma bara. Don haka gwmanati ta duba, ta ga dole wannan abubuwa a taka masu birki.’’

 

Ya ƙara da cewa tsarin zai tsaftace harkokin kasuwanci a jihar, musamman yadda aka saba samun masu yi wa ƴan kasuwa zambo domin kwashe masu kuɗi, kuma ana samun irin waɗannan bata gari masu aikata daga kowanne ɓangare.

 

‘‘Za ka ga ana karɓar kayansu da yawa ana cinyewa, kuma su ma daga cikin su ana samun masu cinye wa ƴan kasuwar Kano kaya ko kuɗinsu, to gwamnati ta ga cewa dole ta shiga tsakani domin a kawo kyakkyawan yanayi na kasuwanci’’

 

Kwamitin dai ya tabbatar da cewa rijistar ba ta shafi ƴan wasu jihohin da suke zaune a jihar Kano ba, sannan kwamitin ya kunshi jami’an tsaro na ƴan sanda da DSS da hukumar kula da shige da fice da ƴan kasuwa da kuma shugabannin kungiyar ƴan China masu kasuwanci a jihar Kano, inda ake fatan nan da makonni biyar kwamitin ya mikawa gwamnati rahotansa.

 

Mai Rahoto

Mujahid Muhammad Tasiu

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid November 5, 2024 November 5, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Mutum 25 Sun Rasu Bayan Bullar Sabuwar Annoba a Jahar Sokoto

Attajdid Attajdid November 19, 2024
Isra’ila  Tayi  Sandiyar Mutuwar Fararan  Hula  Guda 500
After 4 year Out of Premier League Jigawa Golden Star Gets New Management  
Majalisar Dattawa ta Amince Tinubu ya Ciyo bashin $2.2bn
The Bauchi State governor, Bala Mohammed, has disclosed that he and others in his government are ready to sacrifice their lives for the people to live
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?