Babban daraktan ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sheda an sami shahidai guda 4 da wanda aka jikkata mutane 18 a wani sabon kisan gilla da Isra’ila ta yi a makarantar Salahul Din ana yi Allah wadai da mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa a Gaza sannan an yi kira ga kasashen duniya da Isra’ila ta daina kai hari kan fararen hula a Gaza.

Makarantar Salah al-Din ita ce cibiyar kuma mafaka ta goma da sojojin Isra’ila suka jefa bama-bamai tun farkon wannan wata ya kara da cewa Mun yi kira da a samar da asibitocin fage a yankin Gaza ba tare da wani amfani ba Sojojin mamaya sun riga sun yi shirin kai harin bam a kowace makaranta tare da shirye-shirye.

Da fakewa da bayanai marasa tushe balle makama Sojojin Isra’ila na da wani shiri na rusa al’ummar Palastinu da kuma halaka su Sojojin mamaya sun yi amfani da jefa yankin cikin yunwa da hana shigo da kayayyaki.
At-tajdid News.




