A Abuja Wasu musulmai masu kishin addinin muslunci sun yi kira da babbar murya ga gwamnatin tarayya kan batun bashi da ruwa. Wani dalibin ilmi kuma dan kasuwa, Aminu Abdullahi Chubado ya koka a kan yadda aka sa ruwa a tallafin NYIF da za a ba matasa.
Malam Aminu Chubado ya bayyana kokensa a dandalin X watau Twitter, yake cewa riba ta hana shi neman tallafin. Idan za a tuna, Nairametrics ta ce gwamnati ta kawo wani tsarin agazawa matasa da jarin N110bn domin a iya bunkasa kasuwancinsu.
BASHI DA RUWA A TALLAFIN NYIF Sai dai matashin ya bayyana cewa akwai ruwan 5% akan wannan bashi da dan kasuwa zai kara idan har ya tashi biyan bashin. Da mu ka zanta da shi, Mal. Chubado ya bayyana cewa za su so gwamnatin Bola Tinubu ta cire ruwan da ya zama takunkumi gare su. “Na so in nemi tallafin jarin matasa na kasa, sai na duba ka’idoji da sharudan bashin, sai na lura.
Bayan cika duka sharudan, ba zan iya neman bashin ba, saboda kurum akwai ruwa. Ya kamata zababbun wakilanmu su yi wani abin a kan wannan. Aminu Abdullahi Chubado ya kara da cewa Musulunci ya haramta bashi da ruwa a cewar dan kasuwar, malaman musulunci sun nuna rashin halaccin karbar irin dukan wadannan bashi kamar na su NIRSAL.Ganin mafi yawan malamai sun ce haramun ne cin bashi da ruwa, dan kasuwan ya roki shugabanni su kawo tsarin musulunci.
Ana so ‘yan majalisa su cire ruwa Legit ta lura tuni aka fara yin kira ga ‘yan majalisu irinsu Bello El-Rufai su yi yunkuri a majalisa domin a musuluntar da bashin. A dandalin na X, wani Shamsudden Sulaiman Jere ya jawo hankalin mai girma Kashim Shettima da Barau Jibrin kan batun.
Ganin Ministar matasa musulma ce, an yi kira a gare ta cewa a cire ruwan da aka kakaba wajen ba da wannan tallafin kasuwanci.Duk da a wannan kasar tamu mafiyawan mazaunanta musulmaine , Muhammad Karamba ya ce ba a yi la’akari da addini ba a cikin tsarin tattalin arziki kasar.
Legit.
At-tajdid News.




