Yau Juma’ah, 2/8/2024, an shiga cikin wuni na biyu daga cikin wuni goma da aka ce za a yi ana zanga-zangar nuna fushi da gwamnatin tarayyar Najeriya.
Manyan dalilan yin wannan zanga-zangar guda biyu ne: tsadar kayan masarufi da rashin darajar kudi, ko ma rashinsu a hannu, wanda ya jefa mutane cikin halin yunwa da tagayyara; sai kuma rashin tsaro wanda ya sabbabar hasarar rayukka da dukiya, ya kuma hana walwala. Masu zanga-zangar sun ta’allaka wadannan matsaloli da ma wasunsu ga rashin samun kyakkyawan jagoranci.
A cikin Alkur’ani mai girma a cikin Suratun Nahl (surah ta 16), aya ta 112, Allah Madaukakin Sarki Ya yi bayanin abinda ya sa a kan jarabci al’umma da yunwa da rashin tsaro, Ya kuma bayar da mafita.
Allah Ta’ala Ya ce:
(وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا قَرۡيَةٗ كَانَتۡ ءَامِنَةٗ مُّطۡمَئِنَّةٗ يَأۡتِيهَا رِزۡقُهَا رَغَدٗا مِّن كُلِّ مَكَانٖ فَكَفَرَتۡ بِأَنۡعُمِ ٱللَّهِ فَأَذَٰقَهَا ٱللَّهُ لِبَاسَ ٱلۡجُوعِ وَٱلۡخَوۡفِ بِمَا كَانُواْ يَصۡنَعُونَ)
“Kuma Allah Ya buga misali da wata Alkarya (wata kasa) wadda ta kasance cikin aminci da kwanciyar hankali, arzikinta yana zo mata da yawa daga ko ina, amma sai ta kafurce ma ni’imomin Allah, sai kuwa Allah Ya dandana mata tufafin yunwa da tsoro (rashin tsaro) saboda abinda suka zamo suna aikatawa”
A wannan aya zamu fa’idantu da cewar:
1- Da farko wannan Alkarya tana rayuwa bisa tsarin Allah, don haka Ya saukar masu da aminci da kwanciyar hankali , sannan Ya bunkasa tattalin arzikinsu suka wadata.
2- Daga baya sai suka kafurce ma ni’imomin Allah (wadata da zama lafiya), suka saki hanyar Allah suka koma bin son ransu ko son ran wasu. Wannan canji da suka yi ya sa shima Allah Ya canja masu da akasin ni’imomin da Ya yi masu da farko, Ya saukar masu da yunwa da rashin tsaro.
3- Zamu fahimci cewar idan wata kasa ta samu kanta cikin wannan jarrabawa to ya kamata su gane sun saki hanyar Allah ne, sai su koma mata, watau su bi tsarin musulunci a cikin dukkan bangarorin rayuwa, to Allah zai sake dawo masu da wadannan ni’imomi biyu da Ya kwace masu.
Allah Ka bamu ikon gyarawa, Ka kuma yi muna canji kyakkyawa.
Modibbon Gusau.
27/01/1446.
02/08/2024.





Ameen Amen Allah