By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: An katse wutar lantarki a Sudan yayin da dakarun sa-kai ke kai hare-haren jirage sama: Rahoto
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > An katse wutar lantarki a Sudan yayin da dakarun sa-kai ke kai hare-haren jirage sama: Rahoto
News

An katse wutar lantarki a Sudan yayin da dakarun sa-kai ke kai hare-haren jirage sama: Rahoto

Attajdid
Last updated: 2025/09/09 at 7:44 PM
Attajdid Published September 9, 2025
Share
SHARE

An katse wutar lantarki a Sudan yayin da dakarun sa-kai ke kai hare-haren jirage sama: Rahoto

Jiragen sama marasa matuƙa sun kai hari a yankin soja na Wadi Seidna da tashar wutar lantarki ta Al-Markhiyat a birnin Omdurman, kamar yadda kafafen yada labarai na kasar suka ruwaito.

Hare-haren jiragen sama marasa matuƙa da dakarun Rapid Support Forces (RSF) suka kai sun shafi wurare daban-daban a jihar Khartoum ta Sudan, wanda ya haddasa babbar katsewar wutar lantarki, kamar yadda kafafen yada labarai na cikin gida suka ruwaito a ranar Talata.

 

Jaridar Sudan Tribune ta ambaton shaidu tana cewa jiragen sama marasa matuƙa sun kai hari a yankin soji na Wadi Seidna da kuma tashar wutar lantarki ta Al-Markhiyat da ke birnin Omdurman.

 

Harin ya haddasa katsewar wutar lantarki a faɗin birnin, kamar yadda shaidu suka tabbatar.

 

Bidiyon da aka wallafa a kafafen sada zumunta sun nuna yadda taransufoma ta lantarki a tashar ta kama da wuta bayan jerin fashe-fashe.

 

Dakarun RSF sun kuma kai hari a unguwar Al-Kalakla ta Khartoum, inda wata masana’antar soji take, kamar yadda Sudan Tribune ta ruwaito.

 

Har ila yau, an kai hari a garin Al-Jaili, wanda ke dauke da babbar matatar mai ta kasar, kamar yadda aka bayyana.

Ba a samu rahoton asarar rayuka ba.

 

Harin ya biyo bayan kwanaki kadan da sojojin Sudan suka ƙara ƙaimi wajen gudanar da ayyukan soji a Kordofan, tsakiyar Sudan, domin sake karbe iko da manyan birane a yankin da kuma karya takunkumin RSF a birnin Al Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa.

 

Tun daga watan Mayun 2024, Al Fasher ta sha fama da rikici mai tsanani tsakanin sojojin Sudan da RSF, duk da gargadin ƙasashen duniya kan haɗarin tashin hankali a birnin da ke zama cibiyar agaji ga jihohin Darfur guda biyar.

 

RSF da sojojin kasar sun kasance cikin rikici mai tsanani na neman iko tun watan Afrilun 2023, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da jefa Sudan cikin daya daga cikin mafi munin matsalolin jinƙai a duniya.

Fiye da mutum 20,000 sun mutu kuma mutane miliyan 15 sun rasa matsugunansu, kamar yadda alkaluman Majalisar Dinkin Duniya da na cikin gida suka nuna.

 

Sai dai, masu bincike daga Amurka sun ƙiyasta cewa adadin mutanen da suka mutu na iya kaiwa har 130,000.

 

Mai rahoto

Mustapha Garba Usman

You Might Also Like

Nursing Mother Inmate Freed as Jigawa NLC Women’s Wing Clears Her Court Fines

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

Attajdid September 9, 2025 September 9, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

IRAN TA GOYI BAYAN YUNKURIN TSAGAITA WUTA A GAZA

Attajdid Attajdid August 19, 2024
Dakarun Hadaka a Gaza Sun Kai Farmaki Kan Yahudawan sahyoniya 
The Bauchi State governor, Bala Mohammed, has disclosed that he and others in his government are ready to sacrifice their lives for the people to live
Jigawa Commence Distribution of FG Palliative of 59,000 Bags of Rice, Maize Others
DAKARUN ISRA’ILA SUNA CI GABA DA MAMAYAR WURAREN  PALESDINAWA.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?