By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: YAN BINDIGA SUN KASHE HADIMIN GWAMNA DA MATARSA, ‘YAN SANDA SUN MAGANTU
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > YAN BINDIGA SUN KASHE HADIMIN GWAMNA DA MATARSA, ‘YAN SANDA SUN MAGANTU
News

YAN BINDIGA SUN KASHE HADIMIN GWAMNA DA MATARSA, ‘YAN SANDA SUN MAGANTU

Attajdid
Last updated: 2024/08/21 at 8:21 AM
Attajdid Published August 21, 2024
Share
SHARE

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al’amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jaridaKatsina – Wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan Sanusi Ango Gyaza, mai taimaka wa gwamnanKatsina, Malam Dikko Radda a Gyaza, da ke karamar hukumar Kankia.

Gyaza, wanda tsohon shugaban kungiyar malamai ta Najeriya NUT na karamar hukumar Kankia ne, an kashe shi a harin tare da matarsa kamar yadda rahoto ya nuna.’Yan bindiga sun kashe hadimin gwamnaRundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta bakin kakakinta Abubakar Sadiq, ta tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, inji rahoton Leadership.An ruwaito Abubakar Sadiq yana mai cewa, “Eh, muna sane kuma muna kan bincike.

”Jardar Sahara Reporters ta ruwaito cewa ‘yan bindigar sun kashe hadimin gwamna da uwar gidansa a gidansa da ke unguwar Gyaza da ke Kankia a ranar Juma’a.Ayyukan ‘yan bindiga na ta’azzara a Katsina An kuma tattaro cewa a yayin harin, ‘yan bindigar sun sace matarsa ta biyu, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici da jimami. Al’umma sun nuna damuwa game da yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a jihar, inda ayyukan ’yan ta’adda da suka hada da garkuwa da mutane da kashe-kashe ke karuwa.

Da aka tuntubi babban daraktan yada labarai na gwamnan jihar Maiwada Danmallam, bai amsa sakon da aka aikawa lambar wayarsa da aka sani ba har zuwa hada wannan rahoto.

‘Yan bindiga sun kashe dan siyasa a Katsina A wani labarin, mun ruwaito cewa ‘yan bindiga sun kai hari ƙauyen Mairuwa da ke ƙaramar hukumar Faskari a jihar Katsina inda suka kashe wani dan siyasa, Alhaji Lado. Wata majiya da ta bayyana marigayin a matsayin ɗan kasuwa, ɗan siyasa kuma babban manomi, ta ce marigayin an kashe shi ne lokacin da ya ƙi yarda ya bi ƴan bindigan.

Asali: Legit.

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid August 21, 2024 August 21, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
Uncategorized

Jigawa LG Election Holds Peacefully

Attajdid Attajdid October 5, 2024
November 16, 2024
Fashe-fashen na’ura a Labanon ƙaddamar da yaƙi ne: Shugaban Hezbollah
AN SAMU CIMA MATSAYA TSAKANIN MANOMA DA MAKIYAYA KARIM LAMIDO
Ana Saran Za a Cimma Mastaya Akan Tsagaita Da Kuma Musayan Bursunonin Falasdinu da Isra’ila.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?