{"id":4794,"date":"2025-06-20T07:30:11","date_gmt":"2025-06-20T07:30:11","guid":{"rendered":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=4794"},"modified":"2025-06-20T07:30:11","modified_gmt":"2025-06-20T07:30:11","slug":"manhajojin-aika-sako-a-matsayin-makaman-%c9%93oye-ko-an-yi-amfani-da-whatsapp-a-harin-israila-kan-iran","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=4794","title":{"rendered":"Manhajojin Aika Sako a Matsayin Makaman \u0253oye: Ko an yi amfani da WhatsApp a harin Isra\u2019ila kan Iran?"},"content":{"rendered":"<p>Iran ta ce WhatsApp ya fitar da bayanan sirrin masu amfani da bayanan sirri ga hukumomin leken asirin Isra&#8217;ila, yana mai nuni da cewa wannan keta sirrin na iya taimaka wa Isra&#8217;ila wajen kai wasu hare-hare ta sama da suka hallaka wasu manyan jami&#8217;an sojin Iran da masana kimiyyar nukiliyar kasar.<\/p>\n<p>Kafar ya\u0257a labarai ta kasar Iran IRIB ta ruwaito cewa Meta, mamallakin WhatsApp, ya bai wa jami&#8217;an le\u0199en asirin \u0199asashen waje damar &#8220;bibiya da gano&#8221; ma\u0253oyar manyan ma&#8217;aikatan Iran.<\/p>\n<p>Ana zargin bayanan da aka fitar ta WhatsApp sun ha\u0257a da wuraren da jama\u2019a suke da bayanan sadarwa.<\/p>\n<p>Hukumar ta IRIB ta shawarci \u2018yan kasar da su goge manhajoji irinsu WhatsApp da Telegram, inda ta yi garga\u0257in cewa \u201csuna \u0257aukar bayanai da bayyana wurin da mai amfani da shi yake da zarar an kunna wayar hannu ko kuma ha\u0257a ta da intanet<\/p>\n<p>Hukumomin \u0199asar sun kuma bayar da shawarar hana \u0257aukar wayoyin hannu a kusa da wasu wurare masu mahimmanci, tare da yin kira ga \u0257ai\u0257aikun mutane, musamman ma&#8217;aikatan cibiyoyi masu mahimmanci, da su guji amfani da manhajoji marasa tsaro wajen sadarwa.<\/p>\n<p>Meta ya musanta zarge-zargen, yana mai nanata cewa WhatsApp na amfani da kare bayanan sirrin kowanne \u0253angare, kuma baya bin diddigin wuraren da masu amfani da shi suke ko kuma satar bayanan sirri.<\/p>\n<p>A cikin wata sanarwa da CBS News ta fitar, mai magana da yawun Meta ya kira rahotanni da cewa &#8220;\u0199arya&#8221; ce, kuma ya bayyana damuwa cewa Iran na amfani da irin wannan i\u0199irarin a matsayin hujja don toshe damar yin amfani da manhajar tasu.<\/p>\n<p>Garga\u0257in na Iran ya zo ne a daidai lokacin da duniya ke ci gaba da binciken manhajojin sa\u0199onni da ke ikirarin \u0253oye sirrin masu amfani da su. Telegram, wanda ke da&#8217;awar zama jarumin kare sirri, kwanan nan ya fuskanci wani bincike wanda ya bayyana cewa injiniyoyin Rasha ne ke kula da yadda manhajar ke aiki, kuma an gano a baya yana da ala\u0199a da FSB da sashen tsaron kasar.<\/p>\n<p>A baya ma dai Meta ya fuskanci bincike don goyon bayan kamfanin ga Isra&#8217;ila, musamman ta hanyar abin da kungiyoyin kare ha\u0199\u0199in \u0257an\u2019adam suka bayyana a matsayin tsarin mur\u0199ushe abubuwan da ke goyon bayan Falas\u0257inu a fa\u0257in shafuka da manhajojinsa.<\/p>\n<p>Rahoton Human Rights Watch na 2023 ya kawo misalai sama da dubu inda Meta ya cire ko \u0253oye kalaman magoya bayan Falasdinu a Facebook da Instagram.<\/p>\n<p>Wa\u0257annan ayyukan suna bayyana babban tsarin da kamfanonin fasaha na sadarwa ke amfani da su wajen ya\u0257a labarai da manufofin Isra\u2019ila.<\/p>\n<p>Fitar da bayanan da tsarin sanya idanu<\/p>\n<p>Zargin na Iran ya samu kar\u0253uwa a wani \u0253angare saboda al&#8217;amuran da suka gabata inda aka samu satar bayanan mutane a manhajojin da ake cewa suna da tsaro da bayar da kariya.<\/p>\n<p>A 2019, WhatsApp ya shigar da \u0199ara don a tuhumi kamfanin NSO Group na Isra&#8217;ila, yana zargin cewa an yi amfani da manhajarsa ta Pegasus don kutsawa cikin wayoyin masu amfani da manhajar 1,400, ciki har da &#8216;yan jarida da masu fafutuka.<\/p>\n<p>A watan Mayun 2025, wani al\u0199ali na Amurka ya yanke hukunci a kan WhatsApp, inda ya umurci NSO a ya biya diyyar dala miliyan 168, wannan ne hukuncin shari&#8217;a na farko da ya samu wani mai \u0199era kayan leken asiri da laifin keta mutuncin manhajar aika sa\u0199on da aka \u0253oye.<\/p>\n<p>Yayin da NSO ya musanta zarge-zargen, yadda manhajar ta leken asiri ta samu ikon satar bayanan kira, da sakonni, da kyamarori, da na\u2019urar magana, da bayanan wurin da mutum yake, ya haifar da shakku daga jama&#8217;a game da tsaron da ake cewa akwai.<\/p>\n<p>Tuni aka zargi Pegasus da ala\u0199a da ayyukan sa ido da satar bayanai a \u0199asashe sama da 50, inda a 2021 aka bayyana cewa an saci bayanan da suka ha\u0257a da na shugabannin siyasa.<\/p>\n<p>Wani bincike na baya bayan nan da abokan hul\u0257ar OCCRP suka yi ya bayyana damuwa sosai game da amincewa da wata manhajar aika sakonni ta Telegram, duk da cewa ana mata kallon mai adana bayanai.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Rahoton ya bayyana cewa dubban adireshin IP na Telegram da injinan manhajar na \u0199ar\u0199ashin kulawar Vladimir Vedeneev, injiniyan cibiyar sadarwar Rasha wadda tare da sauran kamfanoni suke bayar da bayanan leken asiri, ciki har da FSB da cibiyoyin bincike da ke da ala\u0199a da sojoji.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Ko da yake Telegram yana tallata shi a matsayin mai \u0253oye bayanan kowanne \u0253angare ne, masana sun yi garga\u0257in cewa ka&#8217;idar MTProto ta manhajar ta \u0199unshi bayanan metadata da ba a \u0253oye suke ba, wa\u0257anda za su iya bai wa masu kula da manhajar ikon bin diddigin bayanan na&#8217;ura da ma adreshin IP na masu amfani da ita ba ma tare da karanta sa\u0199onninsu ba.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Fassara bayanai a matsayin dabarun samar da tsaro<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Dangane da \u0199aruwar damuwa game da le\u0199en asiri na \u0199asashen waje da raunin manhajoji, gwamnatoci da dama, ciki har da na Iran, sun tsananta kira ga samar da dokokin fassara bayanan mutane tare da adana su a iyakokin \u0199asashen masu amfani.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Masu fafutuka suna shakkun cewa irin wa\u0257annan manufofin suna rage dogaro ga kayan aikin wajen ajiye bayanai a rumbunan ajiyar bayanai na Amurka, kuma suna \u0199ara sa ido bisa doka kan yadda ake samun dama ko raba bayanai masu mahimmanci.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Misali, Indiya ta bayar da \u0199a&#8217;idojin bayar da kariya ga bayanan wadanda ke tilasta kare wasu rukunin bayanan sirri na mutum, yayin da Hukumar Kare Bayanai ta Turkiyya (KVKK) ta \u0199arfafa hanyoyin aiki da hana fitar da bayanai zuwa kasashen waje.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Wa\u0257annan yun\u0199urin na \u0199o\u0199arin kawo \u0199wararrun fasaha na duniya \u0199arkashin ikon hukumomin \u0199asa, musamman a lokutan rikici ko ya\u0199i, lokacin da ake kallon sadarwar yanar gizo ta zamani a matsayin muhimmiya ga tsaron \u0199asa.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Wata hanyar da aka fi \u0199auna ita ce ha\u0253aka manhajojin aika sa\u0199onni na cikin gida. Iran ta samar da nata manhajojin irin su Soroush, inda Pakistan kuma ta sanar da samar da manhajar gwamnati ta Beep Pakistan a 2023.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Da fari an tsara manhajar ne don sadarwar cikin gida a tsakanin jami\u2019an gwamnatin tarayya saboda damuwar da aka da\u0257e ana fama da ita game da sirrin bayanai da kuma matsalar yanar intanet. Hukumar Fasahar Watsa Labarai ta \u0198asa (NITB) ce ta samar da Beep, wanda ke da manufar samar da hanyar aika sa\u0199onni mai tsaro ta cikin gida don ku\u0253uta daga na waje.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Ana tallata wadannan manhajoji sau da yawa a matsayin mafiya tsaro kuma ba a samun damar kutse a cikin su daga \u0199asashen waje.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>A yanayin da ake ciki a yanzu, inda zarge-zargen leken asiri na kasashen waje da sabbin raunin kayan fasaha ke \u0199ara yawa, garga\u0257in Iran kan rawar da manhajojin aika sa\u0199onni ke takawa a fagen ya\u0199i a yau, na bayyana hatsarin dogaro kan fasahar intanet ta wasu \u0199asashen daban.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Mai rahoto<\/p>\n<p>M.B.S.Gama.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>At-tajdid News.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Iran ta ce WhatsApp ya fitar da bayanan sirrin masu amfani da bayanan sirri ga hukumomin leken asirin Isra&#8217;ila, yana mai nuni da cewa wannan keta sirrin na iya taimaka wa Isra&#8217;ila wajen kai wasu hare-hare ta sama da suka hallaka wasu manyan jami&#8217;an sojin Iran da masana kimiyyar nukiliyar kasar. Kafar ya\u0257a labarai ta [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":2,"featured_media":4795,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"content-type":"","footnotes":""},"categories":[60],"tags":[],"class_list":{"0":"post-4794","1":"post","2":"type-post","3":"status-publish","4":"format-standard","5":"has-post-thumbnail","7":"category-international-news"},"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4794","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=4794"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4794\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":4796,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4794\/revisions\/4796"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/4795"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=4794"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=4794"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=4794"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}