{"id":4273,"date":"2025-02-14T16:06:04","date_gmt":"2025-02-14T16:06:04","guid":{"rendered":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=4273"},"modified":"2025-02-14T16:06:04","modified_gmt":"2025-02-14T16:06:04","slug":"hamas-ta-bayyana-sunayen-israilawa-uku-da-za-ta-saki-gobe-asabar","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=4273","title":{"rendered":"Hamas ta Bayyana Sunayen Isra&#8217;ilawa uku da za ta Saki Gobe Asabar"},"content":{"rendered":"<p>Bayanan hoto,Alexander Troufanov da Yair Horn da kuma Sagui Dekel-Chen duk suna cikin mutanen da maya\u0199an Hamas suka kwasa daga Isra&#8217;ila a ranar da suka kai samame<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Hamas ta saki sunayen mutum uku da take garkuwa da su wa\u0257anda za ta saki gobe Asabar domin yin musaya da Falas\u0257inawan da Isra&#8217;ila ke ri\u0199e da su a wani \u0253angare na ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin \u0253angarorin biyu.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Hakan na zuwa ne bayan kwanakin da aka kwashe ana fargabar wargajewar yarjejeniyar.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Isra&#8217;ilawan da za a sakin su ne: Alexander Troufanov &#8211; \u0257an Isra&#8217;ila mazaunin Rasha, da Yair Horn &#8211; \u0257an Isra&#8217;ila mazaunin Argentina, da kuma Sagui Dekel-Chen &#8211; \u0257an Isra&#8217;ila mazaunin Amurka.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Isra&#8217;ila ta bayyana cewa za ta ci gaba da ruwan wuta a kan Gaza idan ba a saki mutanen a kan lokaci ba.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Ta\u0199addama ta kaure ne bayan da Hamas ta yi barazanar dakatar da sakin mutanen na Isra&#8217;ila bayan zargin Isra&#8217;ilar da karya \u0199a&#8217;idojin yarjejeniyar tsagaita wuta.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Tun bayan fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wutar a ranar 19 ga watan Janairu, Hamas ta saki Isra&#8217;ilawa 16, da \u01b4an \u0199asar Thailand biyar yayin da ita kuma Isra&#8217;ila ta saki Falas\u0257inawa 566 da take ri\u0199e da su a gidajen yarinta.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Ana sa ran Hamas za ta saki &#8216;\u01b4an Isra&#8217;ila 33 da take garkuwa da su a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar, yayin da ita kuma Isra&#8217;ila za ta saki Falas\u0257inawa 1,900.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Ya\u0199i ya turnu\u0199e a Gaza ne tun bayan da Hamas ta kai wani hari kan Isra&#8217;ila a ranar 7 ga watan Oktoban 2023, inda maya\u0199anta suka kashe kimanin mutum 1,200 tare da yin garkuwa da wasu mutum 251.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Tun bayan wancan lokacin, ma&#8217;aikatar lafiya ta Hamas ta ce an kashe sama da mutum 48,230 sanadiyyar luguden wuta da Isra&#8217;ila ta ri\u0199a yi a Gaza. BBC Hausa.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>Mai rahoto;<\/p>\n<p>M.B.S.Gama.<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>&nbsp;<\/p>\n<p>At-tajdid News.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Bayanan hoto,Alexander Troufanov da Yair Horn da kuma Sagui Dekel-Chen duk suna cikin mutanen da maya\u0199an Hamas suka kwasa daga Isra&#8217;ila a ranar da suka kai samame &nbsp; Hamas ta saki sunayen mutum uku da take garkuwa da su wa\u0257anda za ta saki gobe Asabar domin yin musaya da Falas\u0257inawan da Isra&#8217;ila ke ri\u0199e da [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":2,"featured_media":4274,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"content-type":"","footnotes":""},"categories":[59],"tags":[],"class_list":{"0":"post-4273","1":"post","2":"type-post","3":"status-publish","4":"format-standard","5":"has-post-thumbnail","7":"category-news"},"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4273","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=4273"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4273\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":4275,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/4273\/revisions\/4275"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/4274"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=4273"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=4273"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=4273"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}