{"id":3295,"date":"2024-10-03T08:48:52","date_gmt":"2024-10-03T08:48:52","guid":{"rendered":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=3295"},"modified":"2024-10-03T08:48:52","modified_gmt":"2024-10-03T08:48:52","slug":"israila-tana-luguden-wuta-ta-sama-a-beirut-bayan-da-take-fama-da-wata-mummunar-tarjiya-daga-dakarun-hezbollah","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=3295","title":{"rendered":"Isra&#8217;ila Tana Luguden Wuta ta Sama a Beirut Bayan da take Fama da Wata Mummunar Tarjiya daga Dakarun Hezbollah"},"content":{"rendered":"<ol>\n<li><em>Isra\u2019ila ta kai harin bam a tsakiyar birnin Beirut da sanyin safiyar Alhamis, inda ta kashe akalla mutane shida, bayan da sojojinta masu mamaya suka ga mafi munin rana a gagarumin artabun da ba su taba irinsa ba a fagen daga tsakaninsu da kungiyar Hezbollah ta Lebanon a cikin shekara guda.<\/em><\/li>\n<li><em>Shaidu sun ba da rahoton jin karar fashewar wani katon bam kuma wata majiyar tsaro ta ce Isra&#8217;ila ta kai hari kan wani gini da ke tsakiyar birnin Beirut a unguwar Bachoura da ke kusa da majalisar dokokin kasar, harin da Isra&#8217;ila ta kai a kusa da ofishin gwamnatin Lebanon.<\/em><\/li>\n<li><em>Akalla mutum shida ne suka mutu sannan bakwai suka jikkata, in ji jami&#8217;an kiwon lafiya na kasar Lebanon.<\/em><\/li>\n<li><em>Wani hoto da ake yadawa a kafofin WhatsApp a kasar Lebanon ya nuna wani gini da ya lalace sosai tare da cin wuta a benensa na farko.<\/em><\/li>\n<li><em>Har ila yau, sun kai harin makami mai linzami uku a yankin kudancin Dahiyeh, inda aka kashe shugaban kungiyar Hezbollah Hassan Nasrallah a makon da ya gabata, an kuma ji karar fashewar wasu abubuwa masu karfi kamar yadda jami&#8217;an tsaron kasar Labanon suka sanar.<\/em><\/li>\n<li><em>Yankunan kudancin kasar sun fuskanci hare-hare sama da goma na Isra&#8217;ila a ranar Laraba.<\/em><\/li>\n<li><em>Hukumar kula da bala&#8217;o&#8217;i ta kasar Lebanon ta fada a baya cewa mutane 1,928 Isra&#8217;ila ta kashe a kasar tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.<\/em><\/li>\n<li><em>Gwamnatin Amurka ta ce an kashe wani Ba\u2019amurke dan asalin garin Dearborn a jihar Michigan, a kasar Labanon, inda abokin mutumin da makwabtansa suka ce an kashe shi ne a wani harin da Isra\u2019ila ta kai ta sama.<\/em><\/li>\n<li><em>Kakakin Fadar White House ya ce &#8220;Muna matukar bakin ciki da rasuwar Kamel Ahmad Jawad, kuma muna mika ta&#8217;aziyyarmu ga &#8216;yan uwansa da abokan arziki. Mutuwar tasa wata abar takaici ce, haka ma mutuwar fararen hula da dama a Lebanon.&#8221;<\/em><\/li>\n<li><em>Tun da farko dai, kakakin Ma&#8217;aikatar Harkokin Wajen Amurka, da aka tambaye shi game da rahotannin mutuwar wani Ba&#8217;amurke a Lebanon, ya ce: &#8220;A fahimtarmu ne cewa mazaunin kasar ne na dindindin bisa tsarin doka, ba wani Ba&#8217;amurke ba (wanda aka kashe a Lebanon) amma duk da haka muna mika ta&#8217;aziyyarmu ga &#8216;yan uwa.&#8221;<\/em><\/li>\n<li><em>Yakin da Isra&#8217;ila ke yi a Zirin Gaza, wanda yanzu ya shiga kwana na 363, ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa akalla 41,638. Bugu da \u0199ari, sama da mutane 1,928 ne suka mutu a wani munanan hare-haren da Isra&#8217;ila ta kai a Lebanon.<\/em><\/li>\n<li><em>At-tajdid News<\/em>.<\/li>\n<\/ol>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Isra\u2019ila ta kai harin bam a tsakiyar birnin Beirut da sanyin safiyar Alhamis, inda ta kashe akalla mutane shida, bayan da sojojinta masu mamaya suka ga mafi munin rana a gagarumin artabun da ba su taba irinsa ba a fagen daga tsakaninsu da kungiyar Hezbollah ta Lebanon a cikin shekara guda. Shaidu sun ba da [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":2,"featured_media":3296,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"content-type":"","footnotes":""},"categories":[60],"tags":[],"class_list":{"0":"post-3295","1":"post","2":"type-post","3":"status-publish","4":"format-standard","5":"has-post-thumbnail","7":"category-international-news"},"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3295","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=3295"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3295\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":3297,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/3295\/revisions\/3297"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/3296"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=3295"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=3295"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=3295"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}