{"id":2932,"date":"2024-09-04T20:41:05","date_gmt":"2024-09-04T20:41:05","guid":{"rendered":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=2932"},"modified":"2024-09-04T20:41:06","modified_gmt":"2024-09-04T20:41:06","slug":"yadda-maya%c6%99an-boko-haram-suka-kashe-mutane-goma-a-garin-mafa-na-jihar-yobe","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/?p=2932","title":{"rendered":"Yadda Maya\u0199an Boko Haram Suka Kashe  Mutane Goma a Garin Mafa na Jihar Yobe"},"content":{"rendered":"\n<p>Harin dai na ramuwar gayya ne kan zargin kisan da \u2018yan banga a Mafa suka yi wa wasu maya\u0199an Boko Haram biyu, kamar yadda rundunar \u2018yan sandan yankin ta bayyana.<\/p>\n\n\n\n<p>\u0198ungiyar Amnesty International ta ce mutum 127 ne suka mutu sakamakon harin da wasu &#8216;yan bindiga da ake zargi maya\u0199an Boko Haram ne suka kai a garin Mafa da ke jihar Yobe a Arewa Maso Gabashin Nijeriya.Ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Talata a Abuja, babban birnin \u0199asar.<\/p>\n\n\n\n<p>Sai dai mai magana da yawun rundunar &#8216;yan sanda na jihar Yobe, Dungus Abdulkarim, ya ce kawo yanzu ba su tabbatar da adadin wa\u0257anda suka mutu ba, ko da yake wani jami&#8217;i a garin Bulama Jalaluddeen ya ce adadin ya kai mutum 81 Dungus ya ce maya\u0199an Boko Haram sun yi ramuwa ne kan kisan da suke zargi &#8216;yan banga sun yi wa wasu maya\u0199ansu biyu.<\/p>\n\n\n\n<figure class=\"wp-block-gallery has-nested-images columns-default is-cropped wp-block-gallery-1 is-layout-flex wp-block-gallery-is-layout-flex\">\n<figure class=\"wp-block-image size-large\"><img loading=\"lazy\" loading=\"lazy\" decoding=\"async\" width=\"1024\" height=\"576\" data-id=\"2934\" src=\"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1-1024x576.jpg\" alt=\"\" class=\"wp-image-2934\" srcset=\"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1-1024x576.jpg 1024w, https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1-300x169.jpg 300w, https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1-768x432.jpg 768w, https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1-860x483.jpg 860w, https:\/\/attajdidnews.com.ng\/wp-content\/uploads\/2024\/09\/IMG-20240904-WA0025-1.jpg 1080w\" sizes=\"auto, (max-width: 1024px) 100vw, 1024px\" \/><\/figure>\n<\/figure>\n\n\n\n<p>&#8220;Maya\u0199an Boko Haram kimamin 150 \u0257auke da manyan bindigogi da na&#8217;urorin harba bindigogi a kan babura fiye da 50 sun kai hari a Mafa ranar Lahadi. <\/p>\n\n\n\n<p>Sun kashe mutane da dama tare da \u0199ona shaguna da gidaje, sai dai har yanzu ba mu tantance yawan mutanen da suka mutu ba,&#8221; in ji Abdulkarim Dungus.Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi Allah wadarai da harin, sannan ya bu\u0199aci jami&#8217;an tsaro su \u0199ara \u0199aimi wajen mur\u0199ushe masu tayar da \u0199ayar baya.Jihar Yobe dai na \u0257aya daga cikin jihohi uku da suka kwashe tsawon shekaru 15 suna fama da hare-haren maya\u0199an Boka Haram.<\/p>\n\n\n\n<p>Dubban &#8216;yan Nijeriya ne aka kashe tare da raba sama da miliyan biyu da matsugunansu.<\/p>\n\n\n\n<p>Asarar rayuka masu yawaWani jami&#8217;in sojin Nijeriya da ya raka kwamandan rundunar sojoji a jihar ta Yobe zuwa Mafa, ya ce an dasa bama-bamai a hanyar shiga garin, sai dai sojoji sun yi nasara kwance su.\u201cMun samu gawawwaki 37 wa\u0257anda muka kai su babban asibitin Babangida,\u201d in ji jami\u2019in wanda ya bu\u0199aci a sakaye sunanshi saboda ba shi da izinin yin magana da manema labarai.<\/p>\n\n\n\n<p>Wani mazaunin garin Modu Mohammed, ya ce mazauna garin da dama sun \u0253ace, kana ya \u0199iyasta adadin mutane fiye da 100 da suka mutu.Ya \u0199ara da cewa, har yanzu akwai gawawwaki a cikin daji. <\/p>\n\n\n\n<p>(TRT Afarka Hausa).<\/p>\n\n\n\n<p>At-tajdid News.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Harin dai na ramuwar gayya ne kan zargin kisan da \u2018yan banga a Mafa suka yi wa wasu maya\u0199an Boko Haram biyu, kamar yadda rundunar \u2018yan sandan yankin ta bayyana. \u0198ungiyar Amnesty International ta ce mutum 127 ne suka mutu sakamakon harin da wasu &#8216;yan bindiga da ake zargi maya\u0199an Boko Haram ne suka kai [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":2,"featured_media":2935,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"content-type":"","footnotes":""},"categories":[1],"tags":[],"class_list":{"0":"post-2932","1":"post","2":"type-post","3":"status-publish","4":"format-standard","5":"has-post-thumbnail","7":"category-uncategorized"},"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/2932","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=2932"}],"version-history":[{"count":1,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/2932\/revisions"}],"predecessor-version":[{"id":2936,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/2932\/revisions\/2936"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/2935"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=2932"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=2932"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/attajdidnews.com.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=2932"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}